GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Nov 15, 2011

ARBA'UNA HAADITH (33) HADISI NA TALATIN DA UKU


An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Da za a bai wa mutane dukkan da'awarsu, da waɗansu sun yi da'awar dukiyar waɗansu da jininsu, sai dai hujja tana kan mai da'awa, rantsuwa kuma a kan wanda ya yi musu." Baihaƙi ne ya rawaito shi a cikin littafinsa Sunan (J 10/ sh 252). Wani sashi na hadisin yana cikin Bukhari da Muslim.

SHARHI
Ma‘ana, da duk da'awar da mutane za su yi, za a ɗauka a ba su wannan abin da suka yi da'awa, misali in sun ce kaza namu ne, a ba su, ba tare da shaida ba, ba tare da an bincika
ba, "....da waɗansu sun yi da'awar dukiyar waɗansu...." da sun yi da‘awar jinin wasu. Sai Annabi () ya ce, "....sai dai hujja tana kan mai da’awa...." Ma'ana; ana neman mai da'awa da ita, wanda kuma ake nema da ya yi rantsuwa, shi ne wanda ya yi musu. Abin nufi, idan na zo na ce motar da wane yake hawa tawa ce, ni na ba shi rance, ya hana ni, wannan abin da na yi, da'awa ce, to a shari‘ance kafin a yi hukunci, ana neman in kawo shaida. Idan na kawo shaidu, suka tabbatar da wannan tawa ce, dole a karɓe wannan mota a ba ni, a shari'ance. Shi kuma in ya yi inkari, ya ce sam! duk da shaidar nan da na zo da ita bai yarda ba, to sai ya yi rantsuwa, don a tabbatar da haka ne. Wato dai kullum mai da'awa shi ne ake bin
bashin dalili, idan mutum ya yi da'awar abu kaza haramun ne, shi za a ce ya kawo dalilinsa; idan mutum ya yi da'awar halacci a cikin abin da asalinsa haramci ne, to wannan shi za a nemi ya kawo dalili.
Wannan hadisi asalinsa mai girma ne ƙwarai da gaske, yana shiga babuka da dama, musamman ma babin da ya shafi haddi, babin da ya shafi rigingimu a tsakanin mutane da rigimar dukiya. Hadisin dai yana shiga babi da dama na fiƙihu da babin ma'amaloli.

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...