GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Nov 8, 2011

ARBA'UNA HAADITH (28) HADISI NA ASHIRIN DA TAKWAS

An karɓo daga Abu Najih, shi ne Irbadu ɗan Sariya (RA) ya ce, "Manzon Allah () ya yi mana wa'azi, wa'azi mai isarwa, zukata suka tsorata, ldanu suka zubar da hawaye. Sai muka ce da shi, "Ya Manzon Allah ()! Kamar wa'azin mai ban kwana? To ka yi mana wasici." Sai ya ce, "Ina muku wasici da jin tsoron Allah, da kuma ji da bi, ko da bawa ne ya zama shugaba a gare ku. Lallai wanda ya rayu a cikinku, da sannu zai ga saɓani mai yawa. Na umarce ku, ku riƙe sunnata, da sunnonin halifofi shiryayyu, ku riƙe ta da hakoranku (fiƙa), ku kiyayi fararrun al'amura, domin kowace bidi'a ɓata ce. Abu Dawud (#4607) da Tirmizi (#2676) suka rawaito shi, Tirmizi ya ce, wannan hadisi ne mai kyau, ingantacce."


SHARHI
Annabi () ya kasance yakan yi wa sahabbai wa'azi daga lokaci zuwa lokaci, idan hakan ta kama. A wata ruwayar ta hadisin, aka nuna wannan wa'azi Annabi () ya yi musu shi ne bayan sallar Asuba. An kammala sallar sai ya yi wa'azi. Wani lokacin idan ya so ya yi musu wannan wa'azin, yakan hau kan mimbarin juma'a ya faɗakar da su, don a nuna maka ba wai sai juma‘a ne kawai ake hawa mumbarin juma'a ba. Duk lokacin da buƙata ta kama, za ka faɗakar da al'umma, ka hau mumbari, ka yi Innal Hamda Lillahi ɗinka ya yi. lradu ɗan Sariya ya ce, "Manzon Allah () ya yi mana wa'azi mai isarwa, zukata suka tsorata, idanu suka zubar da hawaye...." a sakamakon wannan wa'azin. Wato wa‘azi mai tasiri kenan, wanda yake ratsa zuciya, ya sa suna kukan zuci, suna kukan idanu. Sai sahabbai suka ce, "Ya Manzon Allah ()!...." wannan wa'azin da kake mana, "....Kamar wa'azin mai ban kwana?" ba mu labari idan Allah zai karbi rayuwarka ne. Wato sun ji wa'azin ya ratsa su, sun ji kamar kalma ce ta mai bankwana, don haka sai suka ce, "....To ka yi mana wasici....“ sai ya ce, "Ina muku wasici da jin tsoron Allah..." tsoron Allah kuwa, shi ne kiyaye dokokin Allah Ta'ala, kuma ina yi muku umarni da ji da bi, ku ji, ku bi, "....ko da bawa ne ya zama shugaba a gare ku...." lallai ku ji abin da ya faɗa, ku yi biyayya dangane da umaminsa, matuƙar bai saɓa wa Allah da Manzon Allah () ba. Wannan tsari kenan na shugabantar al'umma, lokacin da duk ƙasa aka ce ga wani mutum an sa shi ya zama shugaba ga al'umma a musulunci, wajibi ne al'umma su yi masa ɗa'a, sai fa idan ya yi umarni da sabon Allah ne, to sai su ƙyale shi, ba za su bi shi ba a cikin abin da ya yi umami da shi na saɓon Allah. Haka ma idan ya yi umami da sabon Manzon Allah() , sai a kyale shi.
Halifofin Annabi su ne, Abubakar Assiddiƙ da Umar bin Khaddab da Usman bin Affan da kuma Aliyu bin Abi-Ɗalib. Waɗannan su ne halifofin Annabi ()! Duk mulkin da ya biyo bayan wannan, sunansa mulki, ba a kiransa halifanci, don su halifofi, halifantar Annabi () suke yi. Idan ka lissafa shekarun da suka yi gaba ɗayansu, za ka ga shekaru talatin suka yi, to waɗannan shekaru talatin ɗin Annabi () ya ce, shi ne lokacin halinfantar Annabta. Daga baya kuma sai Allah ya mayar da abin da ya zama mulki ga wanda ya ga dama. A tarihance sai aka samu waɗannan halifofmin guda huɗu, su suka mamaye shekaun. Wadansu malamai suka ce a'a! waɗannan sahabbai guda huɗu sun mamaye shekaru ashirin da tara ne da wata shida k wata takwas, Alhasan bin Aliyu, bayan Aliyu ya yi shahada, shi ya zama halifa, shi kuma ya yi wata shida ne ki wata huɗu cikon waɗannan shekaru talatin ɗin, da ya ga rigima ta yi yawa, sai ya sauka daga kan shugabancin ya bar wa Mu‘awiya, ya ce masa ya je ya riƙe don a zauna lafiya. Saboda haka idan aka haɗa waɗannan watanni da Hasan bin Aliyu ya yi, wata shida ko huɗu ne, za ka samu shekaru talatin kenan shi ma ya zamanto cikin halifofin Annabi (), amma wannan wata magana ce cikin maganganun malamai. Wannan hadisin yana daga cikin hadisan da suke nuna wajabcin bin sunnar Annabi (). Sai dai mai tambaya zai iya cewa shin akwai bambanci tsakanin sunnar Annabi () da kuma sunnar halifofi masu shiryarwa, ko duk ɗaya ne? Abin da ake nufi, waɗannan sahabbai guda huɗu, idan kansu ya haɗu a kan mas'ala ta addini, to ba za ka ga sun saɓa wa abin da Alƙur'ani ko hadisin Annabi () suka zo da shi ba, shi ya sa aka ce a bi sunnarsu bayan ta Annabi (). To amma idan Abubukar ne (R.A) ya ba da fatawa, ko Usman (R.A) ko Aliyu (R.A) kaɗai ya ba da fatawa, wannan dole ne sai an gwada, idan ta dace da Alƙur'ani da hadisi to shi kenan, amma idan kansu ya haɗu a kan wata mas'ala, to da wuya ka ga sun saɓa wa nassin Annabi ().

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...