GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Aug 6, 2010

ARBA'UNA HADITH {2} HADISI NA BIYU

An karɓo daga Umar (R.A) ya ce, "Yayin da muna zaune a wurin Annabi (ﷺ) wata rana, sai wani mutum ya bayyana gare mu, mai tsananin farin tufafi, mai tsananin baƙin gashi, kuma ba a ganin alamun tatiya tare da shi, kuma a cikinmu babu wanda ya san shi, har ya zauna kusa da Annabi (ﷺ) ya jingina gwiwowinsa guda biyu zuwa ga gwiwowin Annabi (ﷺ), ya ɗora tafukan hannunsa a kan cinyoyinsa, sai ya ce, "Ya Muhammad! Ba ni labari game da musulunci." Sai Annabi (ﷺ) ya ce, "Muslunci, shi ne ka shaida babu abin bautawa bisa ga cancanta, sai Allah, kuma Muhammad  (ﷺ) Manzon Allah ne, ka tsayar da sallah, ka ba da zakka, ka yi azumin watan Ramadan, ka ziyarci ɗakin Allah in ka sami iko." Sai ya ce, "Ka yi gaskiya!" Sai muka yi mamakinsa, saboda yana tambayarsa, kuma yana gasgata shi. Sai ya ce, "Ba ni labarin Imani." Sai ya ce, "Ka yi imani da Allah, da Mala'ikunsa da Littattafansa, da Manzanninsa da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinta da sharrinta." Sai ya ce, "Ka yi gaskiya!" Sai ya ce, "Ba ni labarin kyautatawa." Ya ce, "Ka bauta wa Allah kamar kana ganinsa, idan ba kaganinsa, to shi yana ganinka." Ya ce, "Ba ni labarin alƙiyama." Sai ya ce, "Wanda aka tambaya, bai fi mai tambayar sani ba." Sai ya ce, "Ba ni labarin alamominta." Sai ya ce, "Baiwa ta haifi uwargidanta, kuma ka ga mutane marasa takalma, matsiraita, talakawa, masu kiwon dabbobi, suna tsawaita gine-gine." Sai (mutumin), ya tafi, muka zauna lokaci mai tsawo, sannan sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Ya Umar! Ko ka san mai tambayar nan? Sai na ce, "Allah da Manzonsa su ne suka sani" Sai ya ce, "Haƙiƙa Jibrilu ne ya zo muku don ya koya muku addininku." Muslim ne Ya rawaito shi (#8).


SHARHI

 Wannan hadisi na biyu, an karɓo shi daga Umar ɗan Khaɗɗab. A cikin musulunci Umar ɗan Khaɗɗab shi ne na biyu, mutum na farko shi ne sayyidina Abubakar. Kuma Annabi (ﷺ) ya ce, "Da bayana za a sami Annabi, da ya zamo Umar dan Khaɗɗab."
[Imamu Ahmad da Tirmizi da Hakim suka rawaito shi, Albani ya ce, hadisi ne mai kyau. Duba littafin Albani Silsilatul Ahadisus Sahiha (#327)].
Kuma yana cewa, "A can cikin al‘umman da suka gabata akwai Muhaddasuna-abin da ake nufida Muhaddasuna, wato waɗansu mutane ne da suke da baiwa ta ilhama, waɗanda Allah zai kimsa musu yin wani abu a zuci, sai wannan abin ya dace da shari'ar Allah da ya saukar kan wani Annabi daga cikin Annabawansa. Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "In akwai su a al'ummata, to Umar yana cikinsu." [Imamu Ahmad a cikin Musnad (#339), da Bukhari (#3689) suka rawaito shi]
Dangane da faɗinsa, "....ba a ganin alamun tafiya tare da shi....", alamar tafiya a nan, shi ne a ga gajiyawa tare da shi, in daga nesa yake, sannan a ga ƙura. Babu duk wannan, ga shi kuma ya ce, "....kuma a cikinmu babu wanda ya san shi...." Dukkan abin mamaki ya ƙare a nan wurin. Domin yankin Madina, yanki ne na sahara, in da daga wani ƙauye ya zo, to dole a ga alamar tafiya tare da shi, kamar ƙura, kamar gajiyawa, ko a gan shi da doki, ko alfadari ko rakumi. Amma haka kawai aka ga ya zo, ga tufafmsa fari ƙal, ba abin da ya taɓasu, ga gashin kansa baƙi wuluk, ba alamar tafiya tare da shi, ga shi kuma, "....cikinmu ba wanda ya san shi...." don ba mazaunin Madina ba ne, da mazaunin Madina ne, da mun san shi, saboda mun san kowa. Don kowa ya san kowa a lokacin a Madina,
Dangane da faɗinsa, "....har ya zauna kusa da Annabi (ﷺ) ya jingina gwiwowinsa guda biyu zuwa ga gwiwowinsa, ya ɗora tafukan hannunsa a kan cinyoyinsa....", sai malamai suka yi maganganu daban daban: Waɗansu suka ce wannan baƙon ya ɗora tafukan hannunsa ne a kan cinyoyin Annabi (ﷺ), waɗansu kuma suka ce a‘a! shi bakon ya ɗora hannayensa guda biyu a kan cinyoyinsa, ba a kan cinyoyin Annabi (ﷺ) ba. Wasu sun rinjayar da na ƙarshe saboda shi ne zai fi dacewa da ladabi, kuma shi ne zai fi nuna halin ya kamata. [Duba: Sharhin Sahihi Muslim Na Imam AlNawawi]
Fadin Manzon Allah (ﷺ) cewa"....Ka shaida babu abin bautawa bisa ga cancanta, sai Allah, kuma Muhammad (ﷺ) Manzon Allah ne...." yana nufin ka yarda ba wanda yake cancantar a bauta masa a bayan ƙasa, sai Allah. Ko da an bauta wa wani wanda ba Allah ba, to wannan wanin, bai cancanci bautar ba, an jingina ta ne zuwa ga wanda bai dace da ita ba. Kuma ka yarda babu wanda zai kawo yadda za a yi bautar, sai Annabi Muhammad  (ﷺ). Wannan shi ne ma'anar cewa shi, "....Manzon Allah ne....". Idan ka ɗauki samfurin bauta a wurin wani ba a wurin Annabi (ﷺ) ba, to kamar ba ka yarda da manzancinsa ba ne, ko ka rage wa manzancinsa ƙarfi. Domin dukkan wani abu da yake sunansa ibada ko bauta, wanda za a nemi kusancin Allah da shi, to dole ne ya zama Annabi (ﷺ) ya koyar dashi, in ba Annabi ne (ﷺ)  ya zo da shi ba, kamar an raba aikin Annabi ne an ba wannan mutumin rabi; kamar ana nufin Annabi (ﷺ) bai isar da saƙo gaba ɗaya ba, ya rage wani abu mai falala, bai sanar ba, an sami wani ya zo yanzu yana ƙara wa mutane wani abu. A takaice dai shaidawa Annabi Muhammad (ﷺ) Manzon Allah ne, wannan yana nuna ka bi shi sau-da-ƙafa cikinduk abin da ya zo da shi. Shi ya sa waɗansu malaman suka ce wannan ya ƙunshi ma‘ana ne guda hudu:- Abu na farko: Yi masa ɗa'a cikin duk abin da ya zo da shi, abin da duk ya yi umarni ku bi shi. Abu na biyu: Abin da duk Annabi (ﷺ) ya ba da labari, imma na da, da ya taɓa faruwa, ko abin da zai faru nan gaba a farfajiyar ƙiyama, na labarin wuta da aljannah, dole ne mutum ya gasgata shi, ko abin ya dace da hankalinka, ko bai dace da hankalinka ba, ko abin ya dace da tunaninka, ko abin bai dace da tunaninka ba. Abu na uku: Nisantar duk abin da Annabi (ﷺ)  ya tsawatar, ya ce a rabu da shi. Abu na huɗu: Ka da a bauta wa Allah sai daidai da yadda Annabi (ﷺ) ya zo da shi. To wannan shi ne shaidawa cewa Annabi Muhammad (ﷺ) Manzon Allah ne.
Ma'anar, "....tsayar da sallah...." kuma shi ne sallatar ta a lokacinta, da kiyaye sharuɗɗanta da dokokinta. Sannan kuma mutum ya bayar da zakka ta wajibi. Sannan kuma azumtar Ramadan. Sannan kuma hajji ga wanda ya sami ikon zuwa. Lokacin da Annabi (ﷺ) ya ba shi amsa kan wannan, sai ya ce, "Ka yi gaskiya!" To wannan abin mamaki na biyu kenan, domin abin mamaki na farko, ga wani mutum wanda ba su san shi ba, ga farin tufafi, ga baƙin gashin kai, ba wata alamar tafiya, kuma ba a Madina yake ba, don ba su san shi ba, amma ga shi ya zo wajen Annabi (ﷺ), to daga ina yake? Abu na biyu, galibi idan na yi tambaya, ina yin tambaya ne, don ban san abin ba, amma idan na yi maka tambaya ka amsa, sai na ce "Eh! Ka faɗi gaskiya.", wannan yana nuna na san abin tun kafin in tambaye ka.
A wannan hadisi, Manzon Allah (ﷺ) ya ambaci rukunan imani guda shida: Farko, imani da Allah. Na biyu, imani da Mala‘ikunsa. Na uku, imani da littattafansa. Na huɗu, imani da Manzannin da ya turo. Na biyar, yin imani da ranar tashin alƙiyama. Na shida, imani da ƙaddara. Waɗannan rukunai yadda suke a nan, haka kuma suka zo a cikin ayoyin Alkur'ani, a wani wurin an kawo biyar, a wani wurin kuma an kawo ɗaya 
(Ba musulunci kaɗai shi ne ku juyar da fuskokinku mahudar rana da mafaɗarta ba, musulunci shi ne wanda ya yi imani da Allah da ranar Ƙarshe da Mala'iku da littattafai da Annabawa....) [Baƙara: 177].
 Biyar kenan! saura ɗaya, shi ne can cikin Suratul Ƙamar inda Allah yake cewa,
(Haƙiƙa komai mun halicce shi a kan tsari) [Al-Ƙamar: 49]
Rukunan imani guda shida kenan. Imani da Allah kuma yana da ɓangarori guda uku: Imani da shi ta fuskar Rububiyya, imani da shi da fuskar Uluhiyya, imani da shi ta fuskar Sunaye da Siffofi. Idan ka ce Rububiyya, ka yi imani da Allah ta fuskar ayyukansa, ya kaɗaita a dukkan dangogin aikinsa, kamar kashewa da azurtawa da talautawa da bayar da mulki ko kwacewa da bayar da dukiya ko kwace ta, ko bayar da haihuwa ko hana haihuwa da kawo dare ko kawo rana, da saukar da ruwan sama, da fitar da tsirrai, da bayar da tattalin arzikin ƙasa. Duk waɗannan ayyuka ne na Allah shi kaɗai, babu mai taya shi, domin sama da ƙasa mallakarsa ne, yarda da Allah ta fuskar kaɗaitakarsa a irin waɗannan ayyuka, shi ne yarda da Rububiya.
Na biyu yarda da shi ta fuskar Uluhiyya. Babu wanda za ka bautawa sai shi, dukkan wani dangi na cikin dangogin bauta, haƙƙi ne na Allah shi kaɗai, wani wanda ba Allah ba, ba ya cancanta a bauta masa, wannan ko da Mala‘ika ne, ko da Manzo ne cikin Manzanni, ballantana wanda bai kai darajar Manzanni ba.
Fuska ta uku shi ne, kaɗaita shi ta fuskar sunayensa da siffofinsa. Dukkan sunan da yake sunan Allah ne, to shi kaɗai ya keɓanta da shi, dukkan siffar Allah, shi kaɗai ya keɓanta da ita. Duk abin da ingantaccen hadisi ya tabbatar a matsayin suna na Allah, ko siffa ta Allah, wajibi ne mu yi imani da shi, ba za mu ƙaryata ba, ba za mu karkatar da shi daga ma'anar wannan kalma ba, haka kawai, don ba ta dace da son zuciyarmu ba.
Imani da Mala'iku shi ne imani da su a dunƙule. Akwai wasu siffofl da dukkan Mala'iku sun yi tarayya a kansu, ka yarda da waɗannan siffofin, kamar yadda nassosin Alkur'ani da hadisai suka zo da shi, suka tabbatar. Daga cikin waɗannan, akwai cewa Mala'iku ba a siffata su da cewa maza ne ko mata. Kamar yadda a cikin aljanu akwai maza da mata, Mala'iku ba haka ba ne, su jinsi ɗaya ne babu mata a cikinsu. Siffa ta biyu, mutum ya yarda Mala'iku wata runduna ce mai tarin yawa, wadda babu wanda ya san yawanta sai Allah, Allah ya ce,
(Ba wanda ya san rundunar Ubangijinka sai shi) [Suratul Muddassir: 31].
Siffa ta uku: Ubangiji ya ba wa Mala'iku ƙariln jiki, ya ba su kuma girman halitta. Annabi (ﷺ) ya ce, "Na ga Mala'ika Jibril a daren da aka yi isra'i da ni, a wannan lokaci na gan shi yana da fuffuke ɗaiɗai har guda ɗari shida. [Bukhari (#4857) da Muslim (#174) suka rawaito shi] Kowane fuffuke ɗaya zai iya rufe dukkanin sama, ta yadda in mutum zai ɗaga kansa sama, ba zai iya hango sararin samaniya ba. Abin da yake nuna karfinsu kuwa shi ne an tura Mala'ika ya zo ya ɗauki gari ɗaya, ya tunɓuko shi gaba-ɗaya, ya halakar da gari guda shi kaɗai. Ko Mala'ikan ya yi tsawa, gari guda ya narke, ko al'umma guda ta tafi babu ita. Wannan shi yake nuna ƙarfinsu! Sannan mutum ya yarda cewa, duk inda Mala’iku suke, ba sa saɓa wa Allah.
 (Ba sa saɓa wa Allah a kan duk abin da ya umarce su, kuma suna aikata dukkan abin da aka umarce su) [Suratut Tahrim: 6]
Siffa ta gaba; mutum ya yarda Mala'iku suna bauta ne tsantsa, ba sa saɓo, bauta suke yi dare da rana. Allah ya cece;
 (Suna tsarkake Allah dare da rana ba sa yanke wa) [Suratul Anbiya'i: 20]
Kashi na biyu, shi ne ka yi imani da su tafiran (a rarrabe). Dukkan wanda nassin Alkur'ani ya tabbatar da shi, ko hadisi ya tabbatar da shi, aka faɗe shi da aikinsa, to sai ka yi imani da shi da wannan sunan nasa da aikinsa. Kamar Jibril, sunansa ya zo a cikin Alkur'ani, Mika'il sunansa ya zo a cikin Alkur‘ani, inda Allah yake cewa,
(Duk wanda ya zama maƙiyin Allah da mala'ikunsa da Jibril da Mika'il to Allah maƙiyin kafirai ne) [Suratul Baƙara: 98]
Ka ga a nan, an fadi Jibrila da Mika‘il. Aikin Mala'ika Jibril shi ne kawo wahayi, Mika‘il kuwa aikinsa shi ne koro iskar da take ɗauke da girgije na ruwan sama, da zubo da ruwan saman, da kuma fitar da tsirrai. Sannan akwai mala'ika Israfil, aikinsa shi ne busa cikin ƙaho a ranar tashin Alƙiyama, idan ya yi busa kowa zai mutu, sannan ya sake yin busa a farfaɗo. Allah ya ce,
(Kama aka yi busa a cikin ƙaho, sai duk wanda yake sama da ƙasa ya sume, sai dai wanda Allah ya ga dama, sannan a sake wata busar a cikinsa (ƙahon) sai ga su a tsaitsaye suna jiran tsammani) [Azzumarz 68].

Ya tabbata a cikin hadisi ruwayar Muslim [#769] Annabi (ﷺ) yana yin sallar dare, a cikin sallar daren yana yin addu'ar buɗe sallah, bayan ya yi kabbara, yana cewa, "Ya Allah, Ubangijin Jibrilu da Mika'il da Israfil, mahaliccin sammai da ƙassai...' Sai Mala'ikan mutuwa, wannan sunansa Mala'ikan Mutuwa ko a AIƙur'ani da cikin hadisin Bukhari [#3407] da Muslim [#2372] sunansa Malakul Maut. Hadisin da yake cewa sunansa Azra’ilu bai tabbata ba, hadisi ne mai rauni, don haka sunansa Malakul Maut. Allah yana cewa,
 (Ka ce, "Mala'ikan mutuwa yana ɗaukar ranku wanda aka wakilta gare ku.") [Assajda 11]
 Daga nan sai Malik, Mala'ikan da ke tsaron wuta: Allah ya ce,
(('Yan wuta) suka yi kira, "Ya Malik! Ubangijinka ya kashe mu mana ") [Azzukruf 77]
Daga nan akwai Munkar da Nakir.
To ka ga wannan duk sunayensu ya tabbata ta fuskar nassi. Amma duk Mala'ikan da ba a san sunansa ko aikinsa ba, sai ka yi imani da shi.
Dangane kuwa da imani da littattafan Allah, Allah (SWA) ya ambata mana guda hudu kacal daga cikin littattafan; su ne, Zabura ta Annabi Dawud, Attaura ta Annabi Musa, Injila ta Annabi Isa, sai Alkur'ani na shugaban halitta Annabi Muhammad (ﷺ). Ban da waɗannan, sauran Annabawa dai mun san an ba su littafi, amma ba mu san sunan littafin ba, don nassin Alkur’ani bai faɗa ba, hadisi kuma bai faɗa ba. Idan matambayi ya tambaye ka, "Wane littafi aka ba wa Annabi Shu'aibu?" Sai ka ce, "Ban sani ba!" Wanne aka ba wa Annabi Salihu? Ban sani ba! Wanne aka ba Annabi Hudu? Ban sani ba! Wanne aka ba wa Annabi Nuhu? Ban sani ba! Don Allah bai faɗa ba, Manzonsa bai faɗa ba, ya dai ce ya ba su littafi, sunayensu ba mu sani ba, bai kuma wajabta mana mu sani ba, da ana son mu sani, da an saukar da aya, ko bayani cikin hadisi don mu sani, tunda aka kyale, to ba a so mu sani, sai mu kame bakinmu, tunda wahayi ya riga ya yanke, saboda Annabi (ﷺ) ya bar duniya. Imani da Manzanni kuma ya kasu kashi biyu, imani da Manzanni a jumlace, cewa ba wata al'umma, face sai Allah ya turo mata da Manzo. Allah ya ce,
(Babu wata al'umma, face sai da mai gargadi ya wuce a cikinta). [Faɗir 24]
Wannan yana nuna kulawar Allah ga bayinsa, kada ya bar su sakaka, ba su san makoma ba, sai ya turo musu Manzo. Amma manzannin da aka san sunansu, waɗannan guda ashirin da biyar ne, waɗanda Alƙur'ani ya tabbatar, sauran ba mu san sunayensu ba, ba a kuma kallafa mana mu san sunansu ba. Galibi waɗanda muke samun su a cikin littattafan Isra'ilawa kamar Sham‘ulu da Izƙilu, duk wannan Isra'illiyat ne. Amma in ka duba a cikin Alƙur'ani, an kawo maka sunayen Manzanni, an kawo maka goma sha takwas a jere a cikin suratul An'am [83-86] inda Allah yake cewa,
(Waccan hujjarmu ce muka bai wa Ibrahim a kan mutanensa, muna ɗaukaka darajojin waɗanda muka ga dama. Haƙiƙa Ubangijinka mai hikima ne Masani. Mun ba (Annabi Ibrahim) kyautar Ishaƙa da Yaƙub, dukkansu mun shiryar da su, haka ma Nuhu mun shiryar da shi tun kafin su. Daga zuriyar (Ibrahim akwai) Dawud da Sulaimanu da Ayyub da Yusuf da Musa da Haruna, haka nan muka saka wa masu kyautatawa. Da Zakariyya da Yahya da Isa da Ilyas, dukkaninsu salihai ne. Da Isma'il Da Alyasa‘a da Yunusu da Luɗ, dukkaninsu mun fifita su a kan talikai). [Al-an'am: 83-86]
Sha takwas kenan a nan a jere, sauran kuma ka je ka neme su a wasu wuraren daban a cikin Alƙur'ani Mai girma.
Shi kuwa imani da ranar tashin alƙiyama, yana nufin imani da ranar da idan ta zo, za a yi sakamako ga bayi, za a ƙididdige ayyukan bayi, za a yi sakamako da aljanna, ga wanda ya yi wa Allah biyayya, za a yi sakamako da gidan wuta, ga wanda ya saɓa wa Allah Ta'ala.
Shi kuma imani da ƙaddara ya ƙunshi abubuwa ne guda huɗu, wanɗanda in ka yi imani da su a dunule, su ne za su bayar ka yi imani da ƙaddara. Abu na farko, ilimi: cewa Ubangijin Ta'ala ya san dukkanin halittunsa da ayyukansu da inda za su zauna, da kwanakin da za su yi, da sana'o'in da za su yi, tun kafin halittar su, ya san da wannan abu. Na biyu, Ubangiji ya rubuta duk kaikawon da halittu za su yi, ayyukansu, soja da ɗan sanda, da ɗan kasuwa, da malami da ɗan makaranta, wannan tun kafin a halicci duniya da shekara dubu hamsin, Allah ya rubuta wannan ya ajiye, kamar yadda hadisi ya nuna. Abu na uku, ba abin da zai faru a cikin duniyar nan na mutuwa ko na rayuwa, ko na ɗaukaka ko na ƙaskanci, na cuta ko na lafiya, face sai Allah ya ga damar faruwarsa,.domin mulkin Allah ya sha bamban da mulkin sauran jama'a. Abu na huɗu, Ubangiji (SWA) shi ya halicci ayyukanmu tun kafin mu. Ma'ana duk abin da mutum zai aiwatar na dangin alheri ko kishiyar alheri, Ubangiji (SWA) ne ya halicci wannan abin, sai dai kai ɗan Adam kana da zaɓi na ka yi alheri ko ka yi sharri. Allah ya ce,
(Mun shiryar da shi (mutum) hanya, ko dai ya zama mai godiya (ga Allah, wato ya bauta masa) ko kuma ya zama mai yawan kafirci) [Al Insan: 3]
Ba ka kafa hujja ranar tashin alƙiyama ka ce, ai Allah ya riga ya ƙaddara zan yi kaza, tun lokaci kaza, don haka in ya so in yi ɗa'a, ɗa'ar zan yi, in ya so in yi saɓo, shi ne ya ga dama, ni ba ni da zaɓi. Ba za ka ce wannan ba! Don kuwa duk wanda ya ce wannan, to ka ce ya sami bene mai hawa biyu, ka ɗaura masa tsani ya tattaka ya hau. Idan ya hau, sai ka cire tsanin, ka ce to sauko ba tsanin, idan Allah ya ga dama ka karye, in ya ga dama ka sauka lafiya. Ko shakka babu, ba zai yarda da wannan ba. Dole sai ka kawo tsani, ko lifta! To don me zai ƙi bauta wa Allah kuma da kansa ya yi saɓo, ya ce wai Allah ne ya ga dama ya yi. To don haka imani da ƙaddara shi ne imani da waɗannan abubuwa, cewa lallai Ubangiji (SWA) ya rubuta haka, kuma Ubangiji ganin damarsa ne abin da duk ke faruwa a gidan duniya, kuma Ubangiji shi ne ya halicce mu da kuma ayyukanmu gaba ɗaya. Sannan wajen imani da ƙaddara ba a jingina wa Allah (SWA) sharri, kowane lokaci ana jingina wa Allah alheri ne. Alheri da kishiyarsa ɗin duk daga Allah suke, sai dai shi Allah ba a jingina masa sharri, saboda duk abin da Allah ya halitta, babu sharri tsantsa, sai .dai a wurin ɗan Adam, amma ta fuskar Ubangiji (SWA) abun ba sharri ba ne. Yanzu shi ɗan Adam idan aka ɗora masa ciwon kai, ta iya yiwuwa ya fuskance shi a matsayin sharri, amma kuma ya tabbata a cikin hadisi, duk wanda aka ɗora wa wata cuta ko ƙaya mutum ya taka, za ta kankare masa zunubansa. Wannan alheri ne, amma duk da haka ba za ka so ka wuni ka kwana kana zazzaɓi ko kana ciwon kai ba, saboda kai a gare ka sharri ne, amma a wajen Ubangiji alheri ne. Don haka ba a jingina wa Allah sharri, saboda duk abin da ya halitta akwai wani alheri a ɓoye wanda shi ɗan Adam ba zai gano shi ba.
Daga can kuma, dangane da kyautatawa, sai ya ce, shi ne "Ka bauta wa Allah kamar kana ganinsa, don in ba ka ganinsa, to shi yana ganinka...." a wata riwayar, "Ka tsoraci Allah kamar ga shi kana ganinsa a gabanka zai kama ka da azaba in ka saɓa masa."
Waɗannan su ne abubuwa guda uku da Annabi (ﷺ) ya zana a cikin wannan hadisin. Abu na farko Al-Islam. Abu na biyu Al-Iman. Abu na uku Al-Ihsan.
Sai kuma ya ce, "Ba ni labarin alƙiyama." Sai Annabi (ﷺ) ya ce da shi, "Wanda aka tambaya, bai fi mai tambayar sani ba." Abin da yake nufi, shi ne bai san tashin alƙiyama ba, domin sanin tashin alƙiyama al'amari ne da Allah ya keɓanta da shi. Allah shi ya keɓanta sanin yaushe alƙiyama za ta tsaya, ya dai tabbata cikin hadisi cewa ranar juma'a ne za a tashi alƙiyama, amma wacce juma'ar, mai zuwa ko waccan ta gaba, Allahu A'alam! Allah ne kawai ya san wacce juma'a ce. Saboda haka ba wanda ya san ranar da za a tashi alƙiyama, sai Allah.
Dangane da cewa, "Baiwa ta haifi Uwargidanta....", malamai sun yi bayani suka ce, abin da ake nufi da wannan shi ne, musulunci zai haɓaka a buɗe garuruwa, a ci su da yaƙi, a kama kuyangi mata da yawa. Idan mutum ya zo ya auri baiwa ya yi saɗaka da ita, sai ta haihu, ɗan data haifa ɗa ne, ita kuma ta zama baiwa, shi ne abin da wasu malaman suka fassara wannan. [Don ƙarin bayani duba "Fathul Bari" na Imam Ibnu Hajar J. 1 sh. 122 da "Sharhin Muslim" na Imam An-Nawawi j. 1 sh. 132]

Sai kuma ya ci gaba da bayanin alamominta, ya ce, za ka ga mutanen da ƙafarsu ba takalmi, ga su babu tufafin kirki, ga su kuma masu kiwon awaki, za ka ga irin waɗannan mutane daga ƙarshe sun zo suna gasar tsawaitawa wajen gini; wannan yana so
katangarsa ta fi ta wane! In ka ga irin wannan ta faru, to ƙiyama ta kusa zuwa kenan.
Bayan wannan mutum ya gama tambayar Annabi (ﷺ), shi kuma ya ba shi wannan amsa, sai ya tashi ya tafi. Umar ya ce, "....muka zauna lokaci mai tsawo...." sannan sai ya ce da ni, "Ya Umar! ko ka san mai tambayar nan?" Sai na ce, "Allah da Manzonsa ne suka sani." Sai ya ce, "Haƙiƙa Jibrilu me ya zo, don ya koya muku addininku." Ma'ana, Mala'ika Jibrilu ya yi tambaya, ba don shi ba, sai don ku, ku fahimci menene musulunci, ku fahimci ihsani, ku gane alamomin tashin alƙiyama. Don ku ya yi tambayar, don ku sani. Shi ya sa tambaya da amsa, ɗaya ce daga sigogi na yada ilimi tsakanin al‘umma, shi ya sa Alƙur'ani ya zo da ita da yawa, kuma shi ya sa a hadisin Annabi (ﷺ) da dama za ka ga alamar tambaya da yawa, sannan amsar ta zo. To wannan ruwayar haka take, Imamu Muslim ya rawaito.
A wata riwayar da Tirmizi ya rawaito [#2610] a maimakon a faɗi Al-Islam kafin a faɗi Al-Iman sai aka faɗi Al-Iman, sannan aka ambaci Al-Islam daga baya. A wata riwayar daban kuma a wani wurin daga cikin inda Muslim ya rawaito, da aka ambaci Al-Islam ba a kawo Imani ba, sai aka kawo Al-Ihasan, sannan daga ƙarshe aka kawo Al-Iman. Dukkaninsu dai waɗannan abubuwa guda uku mataki-mataki ne daga cikin matakan musulunci. A nan wurin an fassara mana musulunci da ayyukan gaɓɓai ne, kalmar shahada harshe ne ke furta wannan, gaɓɓai ne ke yin salla, zakka, azumi, hajji. Waɗannan ayyuka kuma sun kasu kashi uku: Akwai wanda ake yi da jiki kaɗai, akwai kuma waɗanda ak yi da dukiya kaɗai, akwai kuma na dukiya da gangar jiki. Kalmar shahada harshe k furta ta, sallah gangar jiki ce ke yi, azumi gangar jiki ke yi, wanda ake yi da dukiya kaɗai shi ne zakka ta wajibi, wanda kuma aka haɗa wani ɓangare na dukiya da jiki shi ne aikin hajji, sai ya kasance an mamaye dukkan ayyukan na zahiri. Domin dukkan wani aiki ko dai da gangar jiki da dukiya, ko da dukiya kadai, ko da gangar jiki kaɗai, in dai ayyukan ibada ne. A nan an fassara musulunci da cewa ayyukan zahiri, da aka zo fassara imani, sai aka ambaci dukkan abin da yake ƙuduri na zuci kaɗai, shi ya sa sai wadansu malamai ke cewa, lokacin da duk aka haɗa musulunci da imani a cikin hadisi ko aya, to Islam yana nufin ayyukan zahiri', Al-Iman yana nufin ƙudiri na zuci, to Al-Ihasan shi ne shugaban gaba ɗaya.



(FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN MARIGAYI SHEIK JA’AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).

Mar 14, 2010

ARBA'UNA HADITH {1} HADISI NA FARKO

SAURARI MUQADDIMA DA SHARHIN HADISI NA (1) DAGA BAKIN MARIGAYI SHEIK JAFAR MAHMUD ADAM



An karɓo daga Sarkin Muminai, baban Hafs, Umar bin Khaɗɗabi ya ce, na ji Manzon Allah (ﷺ) yana ccwa,
"Lallai kaɗai, ayyuka suna tare da niyyoyinsu, kuma lallai kowane mutum yana samun sakamakon abin da ya yi niyya
(azuciyarsa). Wanda duk hijirasa ta kasance saboda Allah da Manzonsa, to hijirarsa tana ga Allah da Manzonsa, wanda kuma hijirarsa ta kasance saboda duniya da zai samu, ko don wata mace da zai aure ta, wannan sakamakon hijirarsa na nan kan abin da ya yi hijira zuwa gare shi." Shugabannin masu hadisai ne suka rawaito shi. Su ne, Muhammad ɗan Isma'ila ɗan Ibrahim dan Mugirata (fan Bardizbah Al-Bukhari' Al-Ju'ufiy. (#1, 54). da Abul Husaini Muslimu ɗan Hajjaju ɗan Muslimu Alƙushairiy Annaisaburiy (#1907) a cikin ingantattun littattafansu, waɗanda su ne mafi ingancin littattafai da aka rubuta.
SHARHI

 Wannan hadisi yana ɗaya daga cikin hadisai mafiya shahara daga cikin hadisan Annabi(ﷺ): Mutum daya ne ya ji wannan hadisi daga bakin Annabi (ﷺ), shi ne Umar ɗan Khaddab; mutum ɗaya ne ya ji shi daga Umar ɗan Khaddab, shi ne Alƙama bin Waƙƙas Allaisiyyi; haka ma mutum ɗaya ne ya ji shi daga wajen Alkama, shi ne Muhammad bin Ibrahim Attaimiyyi; mutum d'aya ne tak, ya ji shi daga wajen Muhammad bin Ibrahim Attaimiyyi, shi ne Yahaya bin Sa'id Al-Ansariyyi. Daga kan wannan bawan Allah, Yahya bin Sa'id Al-Ansariyyi ne wannan hadisi ya shahara. Domin shi ɗaya, sama da mutum ɗari biyu ne suka rawaito hadisin a wajensa. Wannan ita ce hanyar da ta inganta cikin hanyoyin wannan hadisi. Wasu malamai sukan rawaito shi daga Sa'ad bin Abi waƙƙas, amma bai inganta ba, wannan ita ce (kaɗai) hanya ingantacciyya da ta tabbata. Daga cikin mutanen da suka ji wannan hadisi a wurinsa, akwai Imamu malik bin Anas, da Ishak bin Rahawaihi, da Ahmad bin Hambal, da Shu'uba, da Sufyan bin Sa'id Assauriy, da Sufyan bin Uyayna.
Imamul Bukhari ya mayar da wannan hadisi ya zamanto shi ne gabatarwar littafinsa Sahihul Bukhari. Bayan bismillah, sai ya kawo wannan hadisin don ya mayar da shi gabatarwa ta littafinsa, domin ya nuna wa mutane cewa, kowane irin aiki da za ka yi, ba shi zamantowa abin ƙirgawa a wajen Allah, sai in ya zamanto ka yi shi da kyakkyawar niyya, kuma domin ya nuna mafi tsadar ikhlasi a cikin ayyuka. Malamai da dama sun yi magana kan matsayin wannan hadisi, har Abdurrahman bin Mahdi yake cewa, "Da zan sami damar wallafa littafi mai babi-babi na hukuncehukunce, to da sai na mayar da wannan hadisi ya zamanto shi ne gabatarwar kowane babi." Imamush. Shafi'i yana cewa, "Shi wannan hadisi shi ne sulusin ilimi gaba daya." Abin da ake nufi da sulusin ilimi, kashi ɗaya bisa ukun ilimi, sannan ya ci gaba da cewa, "Zai iya shiga babi ɗaiɗai har guda saba'in daga cikin babin
fikihu. [Duba: Jami'ul Ulum Wal Hikam Na Ibnu Rajab 1/23. Fathul Bari 1/10 - 11].
Lafazin Hafs da ya zo a wannan hadisi, a larabce, ɗaya ne daga cikin sunayen zaki, sukan ce masa_HaIfs, sukan ce Asad, sukan ce masa Aglab, sukan ce Hizabr. Zaki yana da sunaye daidai har guda ɗari idan ka duba ƙamus. Ana ce wa Umar ɗan Khaɗɗab Abu Hafs, saboda jaruntakarsa, kuma yana alfahari da wannan alkunya ta Abu Hafs, domin Annabi (ﷺ) ne ya yi masa alkunya da cewa Abu Hafsin.
Dangane kuwa da lakabin Amirul Mu’uminina, Umar ɗan khaɗɗab shi ne mutum na farko daga cikin sahabbai wanda suka yi shugabanci a bayan Annabi (ﷺ) da ake yi wa lakabi da Amirul Mu ’uminina (R.A). Dangane da faɗinsa (ﷺ) cewa, "Lallai kaɗai, ayyuka suna tare da niyyoyinsu....", a nan wurin duk aiki ne, ake yi wa niyya ko kuma akwai waɗanda ba a yi musu niyya? Waɗansu malamai sun ce akwai waɗanda ake yi musu niyya, akwai waɗanda ba a yi musu niyya. Abin da ake nufi da 'ayyuka' a nan kuwa, shi ne ayyukan da suka shafi shari'a kai-tsaye, kamar alwala da sallah da zakka da azumi da dukkan aikin da yake ibada ne tsantsa. To irin waɗannan ayyuka su ne suke bukatar niyya. Amma akwai ayyukan da suka shafi dabi'arka ta ɗan Adam ta yau-da-gobe, kamar zama da tashi da kwanciya da kishingiɗa da cin abinci da shan ruwa da yin wanka da sanya tufafi, da dai sauransu. Waɗannan duk sunansu ayyuka, amma ba sa buƙatar niyya. Don za ka zauna, ba wani buƙatar niyyar zama, don za ka tashi, ba buƙatar sai ka yi niyyar tashi. Ashe lafazin ‘ayyuka‘ a nan, ba ayyuka gaba ɗaya ake nufi ba, abin da ake nufi shi ne dukkan ayyukan da suke sharia ce ta ce a yi su. To irin waɗannan ayyuka,
su ne suke buƙatar niyya. [Duba Jami'ul Ulum Wal-Hikam Na Ibnu Rajab 1/ 26].
Hadisin ya yi maganar hijira, abin da ake nufi da hijira shi ne mutum ya yi ƙaura daga garin kafirci zuwa garin musulunci. Wannan shi ne asalin hijira, wannan hijirar wajibi ce, kuma abu ne mai falalar gaske, shi ya sa ko cikin Alkur‘ani Ubangiji Ta'ala
ya kasa sahabban Annabi (ﷺ) kashi biyu, akwai Al-Muhajirun, akwai Al-Ansar. Su Al-Muhajirun ɗin, kullum aka zo kawo labari su ake fara gabatarwa. To irin wannan hijirar, idan mutum yana son ya yi ta, ya samu lada, to dole sai ya kasance ya yi ta domin Allah, kuma ya yi ta domin koyi da Manzon Allah (ﷺ). Wannan shi ne ma'anar fadin Manzon Allah (ﷺ) cewa, "....Wanda duk hijirarsa ta kasance saboda Allah da Manzonsa...." Wani zai iya cewa, to ai ana yin abu ne domin Allah kaɗai, don me aka raɓa Manzon Allah (ﷺ) ba ciki? Ibnul Kayyim a cikin littafmsa Zadul Ma'ad ya fassara wannan hadisi ya ce, faɗin Manzon Allah (ﷺ) cewa, "Wanda duk hijirarsa ta kasance saboda Allah...." yana nufin da tauhidi, cewar, "....da Manzonsa....", yana nufin don ɗa'a ga Manzon Allah (ﷺ). Don haka hijira zuwa ga Allah ita ce, ƙaura zuwa gare shi ta hanyar tauhidi; hijira zuwa ga Manzon Allah (ﷺ) ita ce kaura zuwa gare shi ta fuskar ɗa'a da biyayya, tunda shi ne ya ba da umarnin a yi hijira ɗin, amma ba wai don shi zai ba da lada ba, Yadda ba a bauta wa kowa sai Allah, haka ma ba'a yi wa kowa biyayya ta gaba ɗaya, sai Manzon Allah (ﷺ).
Fadin Annabi (ﷺ) cewa, “....wanda hijirarsa ta kasance saboda duniya da zai samu, ko don wata mace da zai aure ta, wannan sakamakon hijirarsa na nan kan abin da ya yi hijira zuwa gare shi." yana nufin dukkan wanda ya yi hijira daga wani gari zuwa wani gari, ya zamanto abin da ke cikin zuciyarsa shi ne don ya ci ribar abu iri kaza na duniya, to wannan abin shi kaɗai ne abin da wahalarsa ta hijira za ta ƙare a kai, ko ya sami abin ko bai samu ba, ba shi da lada dai a wurin Allah. Haka nan wanda ya yi hijira domin auren wata, shi ma wannan abin shi kaɗai ne abin da hijirarsa za ta faru ta ƙare a kai, ko ya sami auren ta ko bai sami auren ta ba, ba shi da ladan komai a wajen Allah Ta'ala.
Wasu malamai sukan rawaito hadisi cewa, akwai hadisin wani sahabi da ake cewa Muhajiru Ummu Kaisi, wanda yana neman wata baiwar Allah cikin muminai da aure, sai ta yi hijira ta tafl Madina, shi ko da bai da niyyar zuwa Madina, da ta yi hijira shi ma sai ya nade kayansa ya yi hijira, ya taho Madina. To wai sanadiyyarsa ne sai Annabi (ﷺ) ya fadi wannan hadisi. Wannan  bayani bai inganta ba daga Annabi (ﷺ), wannan hadisi ne da'ifi. [Don Karin bayani duba: Fathul Bari 1/10]
A nan wurin da Annabi (ﷺ) ya fadi ayyuka, sai ya buga misali a kan ɗaya daga cikin ayyukan da ake yi musu niyya, sai ya kawo hijira, don kai kuma, ka yi ta kawo sauran ayyukan da za su iya shiga ƙarƙashin kalmar ayyuka. Buga misali ne Annabi (ﷺ) ya yi, abin ya faru, ko bai faru ba, ya buga misali ne da shi. Duk wanda ya yi hijira don Allah, to ga sakamakonsa, duk wanda ya yi hijira don wani abu, sai ya faɗi dangogin abubuwan da mutane ke buƙata a rayuwarsu.
Niyya tana da Ɓangarori guda biyu: Ɓangaren farko, shi ne ɓangaren da ya shafi flƙihu zalla. A nan wurin ana kawo niyya ne saboda rarrabe tsakanin ibada da ibada, kamar rarrabe tsakanin azahar da la‘asar. Idan muka yi la'akari game da waɗannan salloli biyu, za mu ga raka'o'i hudu ake yi, tsarin karatu ɗaya ake yi, siffar da ake yin su duk iri ɗaya ce, abin da yake bambance wannan azahar ce, wannan la'asar ce, shi ne niyya! Saboda haka ana zuwa da niyya saboda bambance tsakanin ibada da ibada; tsakanin farilla da nafila; tsakanin kaffara da bakance, duk niyya ce take bambance waɗannan. Sannan ana zuwa da ita don bambance tsakanin ibada da al'ada. Wani zai iya ƙin cin abinci saboda yana yajin cin abinci, kamar yadda 'yan kurkuku suke a wani gari, ya ce, yau wannan wunin gaba-ɗaya, ba zai ci abinci ba, awa goma sha biyu, an kawo masa abincin safe bai ci ba, an kawo masa abincin rana bai ci ba, har dare ya yi bai ci ba, yanzu ya yi awa goma sha biyu cur. Kai kuma ka tashi da niyyar yin azumi ka yi awa goma sha biyu cur, bambancin da ke tsakaninka da shi a nan, shi ne ta fuskar niyya!  Sai babinta na biyu, shi ne alaƙar niyya ɗin da wanda aka yi aiki dominsa, shi ne Allah. Idan ka yi niyyar sallar azahar a irin tsarin da ake niyya, ka sallaci raka'a huɗu, sallah ta inganta, yanzu sai ka yi niyya kashi ta biyu, kafin maganar lada ta zo, ita ce kyakkyawar niyya tsakaninka da Allah. Ya zamanto ka yi wannan sallar don neman kusancin Allah Ta'ala. To wannan niyya a wannan ɓangarenta na biyu, ba ta shiga babukan fiƙihu, tana Shiga babukan tauhidi ne. Malamai da dama sun yi wallafewallafe a kan niyya ta ɓangaren tauhidi, kuma dukkaninsu suna kafa hujja da faɗin Annabi (ﷺ) a cikin wannan hadisin, "Lallai kadai, ayyuka suna tare da niyyoyinsu...." Wannan ɓangaren fiƙihu kenan! Amma faɗinsa (ﷺ) "....Kuma lallai kowane mutum yana samun sakamakon abin da ya yi niyya (a zuciyarsa)...." wannan ɓangaren da ya shafi tauhidi kenan. [Duba: Jami'ul Ulum Wal Hikam Na Ibnu Rajah 1/28]
Faɗinsa Manzon Allah (ﷺ) cewa, "....Kuma lallai kowane mutum yana samun sakamakon abin da ya yi niyya (a zuciyarsa)...." yana nufin, abin da ka niyyata, shi ne abin da za ka samu. Idan ka yi niyya ta gari tsakaninka da Ubangiji, to Allah zai ba ka lada, idan kuma ba ka da niyya ta gari, to ba ka da lada a gurin Allah. Rashin bambance wannan, zai haifar maka da matsala da dama: Sai a ce mutum ya yi sallah ta isar masa, amma ba lada, sai ka yi mamaki, to saboda ya yi niyyar da ta shafi bambance aiki da aiki, amma niyyar da ta shafi wanda ake yin aikin dominsa, ba ta yi kyau ba.
Malamai suna cewa, idan mutum ya yi aiki, ya nufaci wani a cikin aikin (wato ya yi riya), wannan ba shi da lada a wajen Allah. To amma abin na iya zama kashi biyu: Ta iya yiwuwa, farkon lokacin da za ka yi aikin, ka yi shi domin Allah. Ka tashi niyyar domin Allah, kana cikin aiki kafin ka ƙarasa, sai riya ta shigo. Wannan riyar da ta shigo a tsakiyar sallarka, kafin ka ƙarasa, bayan a farko niyyarka ka yi domin Allah, domin samun kusancin Allah, ba ta isa ta rusa maka aikinka ba, aikinka na nan da cikakken ladanka a wajen Allah.
Don haka sai waɗansu malamai suka ce, ayyuka iri biyu ne, ko dai aikin da yake farkonsa da ƙarshensa suna haɗe da juna, kamar sallah, raka'ar ƙarshe tana hade da ta farko. Suka ce aiki irin wannan, wanda ƙarshensa yana haɗe da farkonsa, to in ka yi kyakkyawar niyya da farko, to ko riya ta shigo, ba ta isa ta rusa maka shi ba, saboda in farkon ya inganta, to ƙarshen ma zai tafi a haka. Amma aikin da ƙarshensa ba ya hade da farkonsa, kamar karatun Alkur'ani; misali kana cikin karatun Alkur'ani da kyakkyawar niyya, ka yi hizifi biyu da kyakkyawan karatunka don Allah sai wani ya zo karatun ya burge shi yana sauraro, sai ka ƙara koda muryarka don ka burge shi, to wannan hizifi biyun da ka yi, ka samu wannan, amma daga ayar da ka fara koɗa muryarka, aikin ya rushe, saboda ƙira‘ar farko, ba ta da alaka da ƙarshenta, inda ka yi kyakkyawar niyya kana da lada, inda ka yi mummunar niyya kuma, ba ka da lada.
Idan kuma ya zamanto aikin ba ka fare shi ba, kana zaune ba ka da niyyar yin sa, sai kawai ka tashi ka yi shi domin wani, to wannan an yi ittifaƙi ba ka da ladan komai a ciki, kuma malamai da dama sun ce musulmi ba shi da wannan dabi'a, duk wanda kuwa ya yi wannan, to ana jin tsoron wannan ya fitar da shi daga cikin musulunci, musamman idan wannan aiki ya zamanto wajibi ne yin sa, kamar sallah. Mutum ba ya sallah kwata kwata, sai ya ga wasu abokansa sun zo, ko ya ga wani mutum ,da yake jin nauyinsa ya zo, ko wanda yake jin kunyarsa ya zo, sai ya tashi ya yi sallah, kawai domin waɗannan kar su tuhumce shi da cewar ba ya sallah, amma a zuciyarsa ba ruwansa da ita, to wannan mutum ba musulmi ba ne, akwai jin tsoron ya shiga ƙarkashin faɗin  Allah Ta'ala,
(Duk waɗanda suke nufin duniya (da ayyukansu) da kayan adonta, to za mu cika musu ayyukansu a cikinta, ba za a tauye musu ba. Su ne waɗanda ba su da komai a lahira sai wuta, abin da duk suka aikata ya rushe, haka abin da suka aikata ya lalace) [Hudu:15 -16].
Ba ya hallata ga mutum ya ce zai yi lafazi da niyya. Niyya abu ne a zuci, har ma da dama a cikin malamai sun ba da fatawar cewa yin lafazi da niyya bidi'a ne. [Duba Jami'ul Ulum Wal Hikam Na Ibnu Rajah 1/63]. Don haka da zarar ka zo sallah ko azumi, abin da ake bukata, shi ne ƙudurcewa a cikin zuciyarka, irin sallar da za ka yi. Azahar ce ko la'asar ce, za ka yi ta ne kai kadai ko jam’i ne, wannan duk za ka haIarta wa zuciyarka ne, ba sai bakinka ya furta haka ba. Da niyyar azumi da niyyar aikin haji, da niyyar sallah da kowace niyya ba a furta ta da baka, ana kudurcewa ne a zuci. Da ka ƙudurce a zuci shi kenan, ka shiga sallah! Sai muƙaranatun niyyar. Wato ya zamanto da ibadar da niyyar sun haɗu da juna, lokacin da za ka shiga cikin ibadar. Misali, lokacin da ka zo za ka yi azahar, ka fuskanci gabas bakinka na ccwa Allahu Akbar! zuciyarka na ƙudurce irin sallar da za ka yi, azahar ce ko la'asar ce. Wannan shi ne muƙaranatun niyya! Haƙiƙaanin al'amarin shi ne, in ka gabatar da niyya a zuci, sannan ka yi kabbara, sallarka ta yi, in ka cuɗanya niyya da kabbara, sallarka ta yi. Abin da ba zai yiwu ba, shi ne ka yi kabbara, sannan kuma daga baya ka shigar da niyya, wannan ba zai yiwu ba.

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...