GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Aug 27, 2022

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

 

SHARHI

Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka dalilan da suke nuna cancantar Allah da bauta shi kaɗai, Da kuma dalilan

da ke nuna kasawar wanin Allah wajen a bauta masa. Zai kawo siffofi da suke nuna cancantar Allah a bauta masa shi kaɗai da siffofi da suke nuna duk wanda ba Allah ba, yana da rauni bai dace a bauta masa ba. Abin da wannan babi da mai bi masa za su nuna mana kenan.

 

************************

Da faɗin Allah;

Shin suna haɗa Allah da wani, wanda ba ya halittar komai, alhalin su ne ake halittawa. Kuma ba sa iya taimaka musu, kuma ko da kawunansu ba sa iya taimakawa? (Al-Araaf 191-192)

_____________________

SHARHI

 

Wannan na nuna gajiyawa. Dukkan wanda za a sanya shi kishiya ga Allah, dukkan matsayinsa, ko yana cikin salihan bayi, ko waninsu, ko yana cikin mala' iku, ko Annabawa, ko aljanu, ko cikin bani Adam, duk wannan sifar ta hada su, ba sa iya halitlar wani abu, su kansu halitta ne na Allah (SWA). Ko da Annabi Isa (ASW) nau'in mu' ujizar da aka ba shi, ba ta yin halitta ba ne mu'jiza ce, ba wai shi ya yi halittar ba. Waɗannan dalilai

ne na nuna gajiyawar wanin Allah. Duk wani wanda ba Allah ba, ba ya taimaka wa wani, haka ma ba ya iya taimaka wa kansa, Yanzu wannan ayar ta nuna mana sittofin gajiyawa uku;

a. Rashin iya halittar wani abu.

b. Rashin taimaka wa kai.

C. Rashin iya taimaka wa wani duk Wani wanda ba Allah ba, waɗannan sifofin sun tabbata a gare shi.

************************

Da faɗarsa

"Waɗanda kuke kira ba Allah, ba sa iya mallakar ko da farar fatar kwallon dabino. Kuma idan kun kira su, ba za Su ji kiranku ba ko da sun ji. ba zä su amsa muku ba, kuma ranar kiyama za a katirce wa shirkarku, babu kuma mai ba ka labarl, Sama da (Allah mai cikakken sani." (Faɗir: 13-14)

­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­­_____________

SHARHI

Ga wata siffa ta nuna gajiyawar duk wanda ba Allah ba. Shi ne ba ya mallakar komai, ko da farar fata ta jikin kwallon dabino. Sannan Ailah (SWA) ya ce duk wanda kuka kira ba zai ji kiram ba. Dalilan da suke hana jin

kira sun hada da mutuwa, na biyu, idan ba kwa gari ko waje ɗaya nan ma ba za ku ji ba. Ko gindin kabari ka je ka kira mai kabari ka ji ya amsa, to wallahi shaiɗan ne ya ke damfarar masu bauta. Idan an kai wani abinci kabari ko aka yi yanka, aka kai wa mai kabari, ba shi yake cin abin ba.

Mai kabarin bai ma san an kawo ba. Masu gadin kabarin, su suke cinyewa, don hakä ba sa so masu wannan aƙidar su gane. Wani lokaci ma har ƙarya suke yi musu, su ce "Ai mai kabari wane yana gaishe ka!"

Wallahi duk ƙarya suke! A ƙarshen ayar sai Allah ya sanya wa abin suna shirka, alhali a farko kira' ya kirawo bautar. Ashe duk wanda za ka kira ba Alah ba shirka ce!

Wannan aya ƙarara ta nuna kiran wanin Allah, ko waye, in dai ba Allah ba, shirka ne kamar yadda Allah (SWA) yake cewa ko da yaushe a Alkur'ani, “Wanin Allah” ka ga ba wai gumaka yake nufi kaɗai ba. A’a duk wanda ka kira a inda ba wanda zai ji sai Allah, wanin nan Annabi ne, mala’ika ne, aljani ne, shehi ne, waliyyi ne, ko ma menene, in dai ba Allah ba ne, ya zama, "Wanin Allah' yin haka babbar shirka ce. Allah ya kiyashe mu.

 

***********************

Ya zo a cikin hadisi sahihi, daga Anas ibn Malik, ya ce, an yi wa Annabi (SAW) rotse ranar Uhud kuma aka balla masa haƙorinsa. Sai Annabi yake cewa, "Ta yaya waɗansu mutane za su rabauta, alhalin sun yi wa Annabinsu rotse a ka? Sai wannan aya ta sauka Allah ya

ce, "Al'amarin (azaba) ba a hannunka yake ba; dan Allah ya ga dama ya karɓi rubansu, ko ya yi musu azaba, domin su azzanumai ne  (Ali -Imrana 128)

­­­­­­­­­­­_______________________

SHARHI

To. Idan an kore wa Annabi mallakar azaba ko rahama, Allan yà ce duk a hannunsa Suke, za a taboatarwa da wani waliyi ko shehi? Kuma wannan hadisi shi ne sababin saukar wannan aya ta Cikin Suuraul Aali-lmraan.

Wannan hadisi, Bükhari |Duba Fathul Bari J / 563 ya kawo shi ba da cikakken isnadi ba, amma Musiim [#1791) ya kawo shi da cikakken isnadinsa. haka nan kuma Ahmad JS/99] da Tirmizi |#5002) da Nasaa’i

duk sun ruwaito shi.

**************************

 

A cikin Bukhari Kuma, an karɓo hadisi daga Abdullahi bin Umar (RA) cewa yaji Manzon Allah (SAW) yayin da ya dago Kansa daga ruku’u a raka’ar ƙarshe ta sallar asubahi, sai na ji yana cewa, Allah ka la’anci Wane da wane Bayan ya ce, “Sami Allahu liman hanidahu, Rabbana Walakal hamdu “  Yana ambaton wasu kafirai da Sunayensu. Sal Allah ya saukar da wannan ayar, "Al’amari ba a hannunka yuke Da. (Aali-Imraan: 128) Bukhari #4069]

­­­­­­­­­­­­­­­­____________________

SHARHI

Wannan hadisi na nuna sanadiyyar saukar ayar shi ne alkunut ɗin da Manzon Allah (SAW) ya yi. Yanzu, wancan sababin ya sha bamban da wannan sababin kuma duk ayar ɗaya ce. Abin da malamai suke cewa, aya ɗaya na iya sauka sau biyu, ko uku, ko kuma sama da haka da dalilai daban-daban. Saboda haka, waɗannan abubuwa guda biyu, dukkansu a Sanadiyar faruwarsu ayar ta sauka, don ta magance abin da ya taru ko Suka faru. a wata fuskar daban, aya ta iya sauka sama da sau ɗaya. Wani abu ya faru ta sauka don dangantakarta da abin, sannan wani lokaci ta Sake sauka don a nuna cewa tana iya magance wannan matsalar, Kamar yadda take iya magance waccan matsalar.

Abin da ayar take nunawa, cewar Annabi (SWA) ba shi da mallakar wani abu a hannunsa na cutar da mutane ko amfanar da su, na yi musu azaba ko rahama. Abin yana hannun Allah (SWA) ne shi kaɗai, ba ya hannun

kowa, babu mai tarayya da Allah (SWA) a cikinsa. Tunda aka ce Annabi ba Shi da shi, Kuma shi ne shugaban halitta, ya nuna kowa ma ba Shi da shi Kenan. Wannan shi ne babban darasin da ke cikin ayar.

Idan muka koma hadisin Anas ibn Malik, me yake nunawa? Ga shi Annabi ya fita yaƙin Uhud har an ji masa ciwo a ka. Abin da wannan yake nunawa shi ne, dukkan wanda ba Allah ba, yakan iya zama ajizi; ya nuna ba shi ne yake ba wa kansa kariya ba kenan. Allah ya kaddara abin ya same shi, kuma lallai ne ya same shi. A wannan lokaci, ba shi da tsimi ko dabara ta kare abin kada ya same shi. Sannan kuma, yana nuna shugabannin jama'a suna ɗaya daga cikin wafanda ake son su fi kowa shan wahala. Ga shi Annabi (SAW) ya fita yaƙi, bai zauna a gida ba, ga shi kuma an fasa masa kai, wannan yana nuna ƙudwatun hasanah. Yadda mabiyansa suka sha wahala, shi ma ga shi yana shan wahala tare da su, har ma ya ti su shan wahala.

 

Hadisin Abduilahi ibn Umar, yana nuna ana iya yin alƙunut a kan kafirai. ldan kafirai sun muzguna wa musulmi, ya halatta a yi musu alƙunut don a la'ance su. Wasu malamai sun fitar da hukuncin cewa ya halatta a ambaci wasu da sunayensu a la'ance su ko bai halatta ba'? Wasu suna ganin ya halatta a ambaci sunan wani a la ance shi, Ka fayyace Sunansa, ba wai ka ambace shi a cikin kafirai ba. Ka ce, "Ya Allah! Ka la' anci wane. Wasu suka ce, in dai ya halatta ka fayyace wani mutum ka la ance shi, to ya halatta ka fayyace wani mutum ka ɗora masa Kalmar kafirci. Domin la'antarsa na biye masa kalmar (kaulasan) wato kafirci.

Domin in dai ka yarda da nagartarsa, ka la a'ance shi? Wasu suka ce, ba za a ambaci wani mutum da sunansa a la'ance shi ba. Domin wanda Annabi ya yi a hadisin, ya yi ne kafin a hana shi. Faɗin cewa, "Laisa laka minal amri shai'un... (Aali-Imraan:128) ya kunshi cewa nan gaba Annabi (SAW) ya daina la'antar kafirai da sunayensu, sai dai a cikin taro. Haka kuma, alkunut ana yin sa a cikin sallar farilla, ba sai a wutiri ba.

 

***************************

A cikin wata riwayar kuma, yana mummunar addu'a ga Safwan ibn Umayya da Suhail ibn Amru da Haris ibn Hisham.

Sai wannan ayar ta sauka, "Al’amari ba a hannunka yake ba...” (Aali Imraan: 128) Bukhari #4070]

__________________

SHARHI

Kuma a cikin ikon Allah (SWA), sai waɗannan mutane suka musulunta, Suka zama cikin manyan sahabbai. Wannan sai ya nuna cewa Annabawa ba su san gaibu ba. In da Annabi (SAW) ya san za su musulunta, ba zai la'ance su ba. Bai daina la'antarsu ba, sai da Allah (SWA) ya ce ya daina. To shi ne hikimar ta cewa ba a nuna wane, Ka la’ance shi, don ka iya la’antarsa yau, gode kuma ya musulunta, sai dai ka la'anci kafirai a cikin taro, Ka ce, ya Allah: Ka la’anci kafirai. Sai la’antar ta fada a kan wanda Allan ya san ba zai musulunta ba. Ga Annabi ya yi adau’a, amma ba’a Karɓa ba, saboda hikimar Allah cewa mutanen za su musulunta, da an karɓa, to da ba su musulunta ba. Hikimar rashin karɓa shi ne nuna cewa mulkin komai gabaɗaya a hannun Allah (SWA) yake, ba ya hannun Annabi (SAW) ballantana waninsa. Kullum ana buga misali da Annabi, ba sai an fadi sauran ba.

*******************

 

A cikin Bukhari, an karɓo hadisi daga Abu Hurairah, ya ce Manzon Allaln (SAW) ya tashi yayin da aka saukar masa da, "Ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci (yaya, Iyaye mata da sauransu).. (Shu’ara:214) Sai ya Kirayi Ƙuraishawa ya ce, Ku fanshi kawunanku (Imani da aiki nagari) don ba zan iya amfanar da ku komai ba a wurin AlIah. Ya Abbas ibn Abdul-Muɗɗalib! Ba zan amtanar da kai komai ba a wurin Allah. Ya Safiyya bint Abdul Muɗɗalib! Ba zan wadatar da ke komai ba a wurin Allah. Ya Fatima bintu Muhammad: Ki roke ni Cikin dukiyata duk abin da kike so a nan gidan auniya), don ba zan amfanar da ke komai ba a wurin Allah (a ranar ƙiyama)."[Bukhari #2753, Muslim #206)

____________________

SHARHI

Bayan ya kira danginsa, sai aka ce ya kirawo kowa da kowa. Wannan yana nuna cewa dangantakar mutum, ba za ta yi masa komai ba a ranar ƙiyama, mutukar bai yi imani da alki nagari ba. Ba fiddau za a yi maka ta tsirar da mutum idan ya mutu ba. Sai dai aiyyuka su kwace shi wajen Allah kamar yadda Allah ya ba da labari a Suuratul Asr. Matular mutum bai yi aiki nagarı ba, in da zai ciyar da fam-taɓa-sama na dukiya, ba za su kwace shi wajen Allah ba. Gwara tun farko ka tsaya ka yi wa kanka gata ka yi imani da aiki nagari yadda addıni ya yi umarni bisa ga dalili ba bisa taƙlidanci ba.

To yanzu Annabi (SWA) kenan an ce ya gargadi danginsa mafiya kusanci, don ba shi da ikon ya kwaci duk wanda bai bi Allah ba, to waye ya isa ya ce zai ƙwaci ɗansa ko babansa ko muridansa Ko makwabtansa?

Amma saboda izgili da rashin sanin ƙimar Manzon Allah (wanimalami yake cewa matsayin waliyyansu da shehunansu ya fi na Annabawa! Da yanzu Annabawa za su dawo duniya, da sun buraci su zamanto muridan Shehi wane! Sannan suke cewa su sun fi ƙarfin aljanna!

Sannan zikirin Juma'a da suke yi ya fí Juma'ar kanta! Irin waɗannan maganganu na hauka, haka suke tara mutane suna faɗa musu. Da ba dan Annabi (SAW) ya roka mana ba, da Allah ya yi fushi ya halakar da mu

gabaɗaya saboda munin iin waɗannan maganganu!

Wannan hadisi Abu Huraira ne ya ruwaito, amma ba shi ne ya halarci ƙissar da kansa ba. Ya samu ƙissar a wurin sahabbai. Ba ka buƙatar ka san wannan sahabin, Domin a ƙa'idar malaman hadisi, jahiltar wanene sahabi, ba ya cutar da kai, domin sahabbai dukkansu adalai ne, Allan ya adalantar da su. Domin wani zai iya cewa wannan hadisi na Makka ne, kuma Abu Hurairah a lokacin bai musulunta ba.

************************

 

A Cikin Wannan Babi Akwai Mas'auloli Kamar Haka.

 

1. Tafsirin ayoyi biyun larko.          

2. Ƙissar yaƙin Uhud.

3. Mun ga alƙunutun da shugaban manzanni ya yi kuma

shugabannin waliyyan duniya (sahabbai) suna cewa amin

4. Waɗanda kuma aka yi wa addu'ar kafirai ne.

5. Cewa waɗanda aka yi wa addu'ar sun yi tabargaza wanda mafi yawan kafirai ba su yi ba. Wato shi ne Sun ji wa Annabi ciwo, da kuma buƙatarsu ta su kashe shi, sannan kuma sun yayyanki wasu ɓangarori na gawawwakin musulmi bayan yaƙi, tare da cewa ya'yan baffanni suke.

6. Duk da haka, Ubangiji ya saukar da, "Al'amari ba a

hannunka yake ba...

7. Faɗar Allah, "..kuma ko ya gafarta musu ko ya yi musu azaba... sai ya karɓi tubansu ɗin, suka kuma yi imani.

8. Halaccin yin alkunut a cikin matsatsi, “Ana yin alkunuti lokacin da kafirai suka tsanantawa musulmai, ko kuma wata musifa da nassin shari'a ya bada izini a yi. Kamar lokacin fari, sai a yi ko wata ya yi khusufi. Amma cuta ta kamar kwalara, ko makamantansu, Annabi (SAW) ya hana a yi musu kunuti. Haka ma wata buƙata taka ta duniya, kamar cin jarrabawa ko neman makaranta, ko neman aure, duk waɗannan ba a yi musu alkunuti.”

9. Halaccin anbaton sunayen waɗanda ake yi wa munanan addu’a da sunan iyayensu.

10. Ana kuma iya la antar wani sananne a cikin alkunut.

11. Ƙissar Manzon Allah (SAW) yayin da aka saukar masa da, "Ka yi wa danginka na kusa gargaɗi.

12. Ƙoƙarinsa (SAW) wajen isar da musulunci inda har akedanganta shi da hauka. Ko da musulmi ne ya yi a yanzu, Za a ce masa haka.

13. Faɗin Manzon Allah (SAW) ga na kusa da shi, da na nesa da shi, "Ba zan iya wadata maka da komai ba a wurin Allah..

har zuwa inda yake cewa, "Ya Faɗimatu yar Muhammad!

Ba zan wadata miki komai ba a wurin Allah. To har idan

Manzon Allah (SAW) ya bayyana haka, kuma shi ne shugaban dukkan manzanni, cewa ba zai iya wadatar da shugabar matan duniya da komai a wurin Allah ba, to in dai mutum ya yi imani da hakan, sannan ya kalli abin da yake cikin zukatan wasu mutane, da suke ganin kansu keɓantattu ne, to zai bayyana a gare shi, yadda tauhidi yake, da kuma yadda addini ya zamo baƙo.

 

2 comments:

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...