GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Oct 26, 2011

ARBA'UNA HADITH (25) HADISI NA ASHIRIN DA BIYAR


An karɓo daga Abu Zarril Al Gifari (R.A) ya ce, "Waɗansu mutane daga cikin sahabban Annabi ()sun ce da shi, "Ya Manzon Allah ()! Ma'abota dukiya sun tafi da lada, suna yin sallar (farilla) kamar yadda muke yi, suna yin azumin (farilla) kamar yadda muke yi, amma kuma suna sadaƙa da sauran dukiyarsu. Sai Annabi () ya ce, "Shin Allah bai riga ya ba ku abin da za ku yi sadaƙa da shi ba ne? Dukkan tasbihi sadaƙa ne, dukkan wata kabbara sadaƙa ce, dukkan wata hamdala sadaƙa ce, dukkan wata hailala sadaƙa ce, umarni da kyakkyawan aiki sadaƙa ne, hana mummunan aiki sadaƙa ne, a gaɓar kowanne daga cikinku akwai sadaƙa"sai sahabbai suka ce "Ya Manzon Allah! Yanzu mutum zai biya buƙatarsa kuma ya zama yana da lada?" Sai (Annabi ) ya ce, "Ku ba ni labari da a ce ya sanya (gaɓar) tasa a cikin haram, shin yana da zunubi? To haka nan in ya sanya ta a halal zai zama yana da lada. Muslim (#1006).

ARBA'UNA HADITH (24) HADISI NA ASHIRIN DA HUDU

An karɓo daga Abu Zarri Algifari (R.A) daga Annabi (), cikin abin da (Annabi) ke rawaitowa daga wurin Ubangijinsa. Lallai Allah Maɗaukakin sarki ya ce, "Ya ku bayina! Na haramta wa kaina zalunci, kuma na sanya zalunci ya zama abin haramtawa a tsakaninku. Ya ku bayina! Dukkaninku ɓatattu ne, sai fa wanda na shiryar da shi, ku nemi shiryarwata, ni kuma in shiryar da ku. Ya ku bayina! Dukkaninku mayunwata ne, sai wanda na ciyar da shi, don haka ku nemi ciyarwata, ni kuma zan ciyar da ku. Ya ku bayina! Kowannenku tsirara yake ba tufafi, sai wanda na suturta, ku nemi suturata, zan suturtar da ku. Ya ku bayina! Kuna yin laifi dare da rana, ni kuma ina gafarta zunubai gaba ɗayansu, ku nemi gafarata, ni kuma zan yi muku gafara ɗin nan. Ya ku bayina! Ba ku i'sa ku cutar da ni ba, ballantana ku ce za ku cutar da ni, ba ku isa ku amfanar da ni ba, ballantana ku ce za ku amfanar da ni. Ya ku bayina! Da a ce na farkonku da na ƙarshenku, da mutanenku da aljanunku, ku kasance a bisa ga zuciyar wani mutum ɗaya cikinku mafi jin tsoron Allah, hakan ba zai kara komai a cikin mulkina ba. Ya ku bayina! Da a ce na farkonku da na ƙarshenku, da mutanenku da aljanunku, ku kasance a bisa ga zuciyar mutum ɗaya mafi fajirci, hakan ba zai rage komai dangane da mulkina ba. Ya ku bayina! Da a ce na farkonku da na

ARBA'UNA HADITH (23) HADISI NA ASHIRIN DA UKU

An karɓo daga Abu Malik, Haris bin Asim Al ash’ariy ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Tsarki rabin imani ne, faɗin Subhanallahi Walhamdulillahi; tana cika mizani, faɗin Subhanallahi da Alhamdulillahi; suna cika, ko (kowace ɗaya daga cikinsu) tana cika abin da ke tsakanin sama da ƙasa; sallah haske ce; sadaƙa huija ce; haƙuri kuma haske ne; Alƙur'ani hujja ne gare ka, ko a kanka. Dukkan mutane suna jijjifi da safe, daga cikinsu akwai mai zuwa sayar da kansa, ko dai ya 'yantar da kansa ko kuma ya halakar da kansa." Muslim (#223) ya rawaito.“

SHARHI

Da Manzon Allah () ya ce, "Tsarki rabin imani ne...." magana mafi inganci dangane da 'tsarki', shi ne abin da

ARBA'UNA HADITH (22) HADISI NA ASHIRIN DA BIYU

An karɓ0 daga Abu Abdullahi, Jabir ɗan Abdullahi Al ansariy (R.A) ya ce, "Wani mutum ya tambayi Annabi () ya ce da shi, "Ba ni labari idan na sallaci salloli na wajibi, na azumci watan Ramadan, na halatta halal, na kuma haramta haram, ban ƙara komai a kan haka ba, shin kuwa zan shiga Aljanna?" Sai Annabi () ya ce, "Eh! (za ka shiga aljanna).") Muslim (#15).

SHARHI

Abin da wannan hadisi yake nunawa, shi ne, idan mutum zai tsaya a kanwajibi kaɗai, ba tare da ya yi mustahabbi ko ɗaya a rayuwarsa ba, in dai ya sauke dukkan wajiban da ake

ARBA'UNA HADITH (21) HADISI NA ASHIRIN DA DAYA

An karɓo daga Abu Amrin ko Abi Amrata, Sufyanu ɗan Abdullahi (R.A) ya ce, "Na ce, "Ya Manzon Allah ()! Faɗa min wata magana a cikin addinin musulunci, wadda ba zan sake tambayar waninka ba game da ita." Sai ya ce, "Ka ce, "Na yi imani da Allah." sannan kuma ka daidaitu." Muslim (#38) ya rawaito.

SHARHI

Wannan hadisi ingantacce ne, Imamu Muslim ne ya rawaito shi. Dangane da bayanin imani da Allah, wannan ya riga ya gabata a baya. A duk lokacin da aka faɗi imani, mun san

ARBA'UNA HADITH (20) HADISI NA ASHIRIN

An karɓo daga Abu Mas'ud, Uƙbatu ɗan Amru Al AnsaIriy Albadariy (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Yana daga cikin abin da mutane suka riska daga zancen Annabtar farko, idan har ka zamto ba ka jin kunya, to ka aikata duk abin da ka so.“ Bukhari(#3483).
             
SHARHI
Wannan hadisi abin da yake nunawa, kamar yadda malamai suke nunawa, shi ne cewa wannan hadisi kamar razanarwa yake, ba wai umami yake ka zama marar kunya ba, a'a! in

ARBA'UNA HADITH (19) HADISI NA SHA TARA

An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (R.A) ya ce, "Na kasance a bayan Annabi () wata rana, sai ya ce dani, "Ya kai yaro! Zan sanar da kai waɗansu jumloli: Ka kiyaye (dokar) Allah, sai kai ma ya kiyaye ka; ka kiyaye (dokar) Allah, za ka samu (Allah) yana yi maka jagora; idan za ka roƙa, to ka roƙi Allah; in za ka nemi taimako, ka nemi taimakon Allah. Ka sani cewa da al'umma za su taru kan su amfane ka da wani abu, ba za su iya su amfanarka da komai ba, sai da abin da Allah ya rubuta maka (cewa naka ne). Idan da al'umma za su taru kan su cuce ka da Wani abu, ba su isa su cuce ka ba, sai da abin da Allah ya riga ya rubuta maka. An riga an cire alƙalami, takardun sun bushe." Tirmizi (#2516) ya rawaito. ya ce, "Hadisi ne mai kyau ingamtacce."

A Wata riwaya wadda ba ta Tirmizi ba, "Ka kiyaye dokar Allah, za ka samu Ubangiji a gabanka (yana
maka jagoranci), ka nemi sanin Allah lokacin da kake cikin yalwa, zai san da kai a lokacin da kake cikin tsanani, ka sani duk abin da ya kuskure maka, da ma can ba a yi shi don ya

Oct 3, 2011

ARBA'UNA HADITH NA (18) HADISI NA SHA TAKWAS

An karɓo daga Abu Zarri (shi ne) Jundubu bin Junada, da Abu Abdurrahman (Shi ne) Mu'azu ɗan Jabal (R.A), Manzon Allah () ya ce, ."Ka ji tsoron Allah, a duk inda kake, ka bi mummunan aikin da ka yi da kyakkyawan aiki, sai (wannan kyakkyawan aikin) ya shafe mummunan, ka ɗabi'anci mutane da kyakkyawar ɗabi‘a." Tirmizi (#1987) ya rawaito, ya ce, hadisi ne hasanun a wani bugun ya ce, hasanun sahihun.

SHARHI
Dangane da faɗin Manzon Allah () cewa, "Ka ji tsoron Allah a duk inda kake....", mun riga mun san menene taƙawa. Ita ce abin da duk aka ɗora maka, ka yi, abin da duk

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...