GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Sep 14, 2011

ARBA'UNA HADITH (17) HADISI NA SHA BAKWAI

An karɓo daga Abu Ya'ala Shaddadu bin Ausi (R.A) daga Annabi () ya ce, "Allah Ta'ala ya wajabta kyautatawa ga kowane irin abu (da mutum zai yi a duniya) idan kuka yi nufin kisa, ku kyautata kisan, idan kun yi nufin yanka (dabba) ku kyautata yankan, kowane dayanku (da zai yi yanka) ya wasa wukarsa, ya hutar da abin yankansa." Muslim (#1955) ya rawaito.
                               
SHARHI
Ma'ana, Ubangiji ya wajabta kyautatawa: Ga kowanne irin abu da mutum zai yi a duniya, ya zamanto ya kyautata shi. Kowanne irin abu, ɗan Adam ne, dabba ne; yana buƙatar
ihsaninka. Don haka sai Annabi () zai kawo misali ɗaya wanda ya shafi ɗan Adam, na biyu kuma wanda ya shafi dabba. Ya ce, "....idan kuka yi nufin kisa...." to ku kyautata kisan. Wato mutum ne ya yi laifin kisa, kuka zo za ku kashe shi, wannan kisan, ku kyautata shi. Abin nufi, ku yi amfani da abin da zai zare ransa nan-take, ba wai ku ɗaure shi da igiya ku rataye ba, ya daɗe bai mutu ba. Wannan idan kuka yi haka, kun saɓa wa wannan hadisin! Ba a ratayewa a musulunci, sai dai a fille kai, ko a yi amfani da dukkan wani abu wanda nan-da-nan zai ɗauke ran mutum cikin ƙanƙanin lokaci, cikin sakan, ko abin da bai kai sakan ba, nan-da-nan ya dauke ran mutum ya huta. Amma ba mutum ya jigata ba kafin ya mutu, wannan bai halatta ba. Sannan kuma ba ya halatta ku yi musla, wato kacancana gawar mutum, ko da kafiri ne kuka zo kashe shi, in dai kun zare masa rai, to ya riga ya gabata, ba sai kun fille kai, kun yanke hannu, kun yanke ƙafa, kun ja a ƙasa, wannan duk ta'addanci ne wanda shari'a ta ce,

(Kada ku yi ta'addanci, haƙiƙa Allah ba ya son 'yan ta'adda) [Al Bakara: 19o]

Amma malamai sun ce, in mutum ya kashe dan uwansa musulmi kisa na ganganci, aka zo za a yi masa ƙisasi, yayin da ya kashe ɗan uwansa musulmi, kuma ya kacancana gawarsa, to shi ma in an zo kashe shi, babu laifi a kacancana gawar don ya zamanto ƙisasi ya tabbata, kamar yadda Allah ya faɗa. Ko kuma sai dai mu kashe shi kaɗai, ba sai mun rama abin da ya yi wa ɗan uwansa ba? Malik da Ahmad bin Hambal da Shafi'i suka ce, ina! Ai yadda ya yi wa ɗan uwansa shi ma sai an yi masa. Wannan shi ne ƙisasi!

Haka idan kun yi nufin yanka dabba kuma, to ku kyautata yankan wannan dabbar ɗin. Sai Annabi () ya fadi yadda za a kyautata yankan, kowane dayanku da zai yi yankan, ya wasa wuƙarsa sosai, kar ya zo ya yi ta dadirawa, ta-ci-ba-ta-ci ba, ya wahalar da rago, kuma bai ɗauke ransa ba. Wannan shi ne ƙashin bayan abin da malamai ke kafa hujja da shi kan cewa addinin musulunci yana kula da ɓangare guda biyu ne, wanda galibi mutane ɓangare ɗaya suke lura da shi, ba sa kula da ɗaya ɓangaren. Suka ce addinin musulunci yana kyautata alaƙa tsakaninka da mahaliccinka; shi ne ka bautata masa shi kaɗai, ka bi umaminsa. Abu na biyu kuma yana kula da kyautata alaƙa tsakaninka da halittu; shi ne ka kyautata musu, ta yadda shari'a ta ce a kyautata musu. Wani sai ya ga cewa a'a! zai yi sallah, zai yi azumi, zai yi zakka, zai yi hajji, zai yi dukkan abin da zai yi, amma tsakaninsa da mutane ba alaƙa mai kyau, ba ya jin tausayinsu, ba ya kyautata musu, zai yi musu ƙarya, zai zalunce su, zai damfare su, zai cinye bashinsu, saboda yana sallar azahar a kan lokaci, shi ya riga ya gama, zai je hajji, zai je umara a kwanakin goman ƙatshe na Ramadan, yana ganin duk abin da ya yi na zalunci wannan umara ta warware shi. Wannan ba zai yiwu ba! Wajibi ka kyautata alaƙa zuwa, ga bayin Allah, mutane ne ko dabbobi ne.

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...