GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Sep 12, 2011

ARBA'UNA HADITH (7) HADISI NA BAKWAI

An Karɓo daga Abu Ruƙayya, (shi ne) Tamim ɗan Ausid Dari (R.A) ya ce, Annabi () ya ce, "Addini nasiha ne!" Sai muka ce, "Ga wa?" sai ya ce, " (Nasiha ne) ga Allah, da Littafinsa, da Manzonsa, da shugabannin musulmi, da dukkan mutane" Muslim ne ya rawaito (#55)

SHARHI

A larabce abin da kalmar annasiha take nunawa, shi ne tace zuciyarka, wanke zuciyarka dangane da wanda aka ce ka yi masa nasiha ɗin. Don haka shi tace zuciya ya sha bamban: Idan ya zamanto tace zuciya ga Allah ne, to kenan kar ka
sanya wa Allah kishiya a cikin zuciyarka, ka wanke zuciyarka gaba-ɗaya ga Allah, ta yadda babu wanin Allah a cikin zuciyarka. Idan ya zamanto nasiha ga littafin Allah ne, to shi ne ka yi imani da littafin, ka yarda babu wani littafin da ya fi shi ginna, ko mutunci a nan duniya, kana ƙoƙarin karanta shi, kana ƙoƙarin fahimtar abin da ke ciki, kana yin imani da dukkan abin da Alƙur‘ani ya kawo na hukunce-hukunce. Wannan ita ce nasiha ga littafin Allah. Nasiha ga Manzon Allah () kuwa, ka wanke zuciyarka ga shi Annabin () wajen ƙauna. Babu wanda kake ƙauna irin yadda kake son Annabi () a nan gidan duniya, babu wanda kake yi wa biyayya irin ta Annabi (), babu wanda ka mayar abin koyinka cikin kowane irin halaye nasa, irin Annabi (). Yadda baka yarda ka sa wa Allah kishiya wajen bauta ba, haka ba ka yarda ka sa wa Annabi () kishiya wajen ɗa'a ba. Duk umarnin da ya kuskura ya ci karo da umarnin Annabi (), to tasa ta ƙare, ka gama da shi, na Annabi () za ka ɗauka. Wannan shi ne nasiha ga Manzon Allah () Nasiha ga shugabannin musulmai, shi ne yi musu ɗa‘a cikin abin da suka yi umarni, wanda bai saɓa wa Allah ba, da gabatar musu da shawarwari da za su taimaka musu, da yi musu addu'a ta gari kan nauyin jama'a da ke kansu, da kokarin faɗakar da su, da jan hankalinsu ta hanyar da za su iya karɓar nasiharka ko maganarka ko fadakarwa.
Nasiha ga dukkan sauran musulmai 'yan uwanka kuwa, ita ce ka so musu irin abin da kake so wa kanka. Duk da wane ya yi maka Barna, ya yi maka ba daidai ba, amma tunda yana son Allah, yana son Manzonsa, sai kake ƙaunarsa a zuci, ko da ba ka faɗa masa ba, kana ƙaunarsa. To idan ka yi haka, ka yi wa 'yan uwanka musulmi nasiha.
Imam Khaɗɗabi ya ce, "Nasiha ita ce son alheri ko nufatar alheri game da wanda ake yi wa nasiha." [Duba: Jami'ul Ulum Wal- Hikam Na Ibnu Rajah 1/207]. Idan ya shafi Ubangiji, to shi ne tsarkake shi daga dukkan tawaya; siffanta shi da dukkan wata kamala; kore masa dukkan wani abin bauta. Idan ya shafi Annabi (), to shi ne jin cewa shi ya fi kowa falala da matsayi (), kuma lallai shari'arsa ta shafe kowace shari'a. Idan ta shafi littafin Allah, to ita ce ɗora littafin Allah a kan kowane littafi. Idan ta shafi ‘yan uwanka musulmai, ita cr so musu abin da kake so wa kanka. Idan ta shafi shugabanni, to ita ce yi musu addu'a ta gari, da fata nagari, da kuma gabatar musu da faɗakarwa ta hanyar da za su iya ji su yarda, tsakaninka da su." [Duba: Jami'ul Ulum Wal-Hikam Na Ibnu Rajab 1/207-212].

Magabata na da, idan za su yi nasiha ga masu mulki, sai su nemi ganin su, gani na musamman, su zauna da su, daga su sai su, su faɗakar da su hukunce-hukuncen Allah, su faɗakar da su sakon Annabi (), In sun gama a ba su kyauta, su ƙi karɓa, su tashi su fita. Sun gabatar da wannan ne saboda sauke nauyin da ke kansu, ba don ba sa son sarakuna ba, sai don kar ya kasance sun cinye ladansu tun daga nan gidan duniya. Idan an flto waje an ce a yi bore, sai su ce, su ba za a yi da su ba, ba sa taɓa yarda a yi bore, domin illar da ke ciki ta ya fi alherin yawa. Yayin da duk wani mai mulki ke zalunci, sai ka ce za ka karɓa da ƙarti, kai kuma kana cikin talakawa ba ku da komai, ku yi zanga zanga, ƙarshen sakamako shi ne a turo 'yan sanda da sojoji su harbe na harbewa, su kashe na kashewa. In kuna da ƙarfi kuma ku kashe wani ɓangare na cikinsu, a ƙona gidaje, a ƙona motoci, a ƙona dukiyoyi, a ƙona ofusoshin gwamnati, daga ƙarshe al'ummar ƙasa ce dai ta yi asara. Saboda haka tayar da hankali ba shi da amfani. Shugabanni idan har musulmi ne, ƙokari ake a yi musu umami da kyakkyawan aiki da hani daga mummuna ta hanyar da za su fahimta.

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...