An karɓo
daga Abu Hamza, Anas ɗan
Malik (R.A), yaron gidan Annabi (ﷺ)
ya ce, Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "ɗayanku ba ya zama mai cikakken imani, har sai ya so
wa ɗan uwansa abin da yake
so wa kansa." Bukhari (#13) da Muslim (#45) suka rawaito
SHARHI
Faɗin
Annabi (ﷺ)
cewa, "....ba ya zama mai cikakken imani....”, wannan yana kore cikar
imani ne, ba wai yana kore asalin imani ba. Irin waɗannan hadisai suna da yawa.
Wani wanda bai fahimce
su sosai ba, sai ya kafa hujja da su bisa cewa, mai aikata saɓo zai iya kafirta, kamar yadda khawarijawa suke yi.
Sai su ɗauki irin waɗannan nassosi, sai su ce, ai duk mai saɓo ya kafurta, kuma in ya kafirta zai dawwama a cikin
wuta, don Annabi (ﷺ) ya kore musu imani;
ya ce, mazinaci a lokacin da yake zina ba shi da imani; Barawo a lokacin da
yake sata ba shi da imani; da sauran irin dangin saɓo da Annabi (ﷺ)
zai faɗa, sai ya kore imanin,
ya ce babu shi. To Annabi (ﷺ) ba yana kore asalin
imani ba ne, yana kore cikar imani ne. Abin da ya sa muka ce ba asalin imani
yake korewa ba, shi ne ai masu saɓo
Allah ya kiraye su da sunan imani, sannan ya ce su tuba. In ba sa saɓo, a ce su tuba? In da kafirtaa suka yi, a sa musu
suna muminai? Allah ya ce, (Ya ku waɗanda
kuka yi imani! Ku tuba, tuba mai zarcewa) [Attharim: 8] Da ba musulmai ba ne, a
kira su da sunan imani? A nan hadisin, da aka ambaci 'ɗan uwa' to 'yan uwantakar musulunci ake nufi, ba
'yan uwantakar jini ba, ba 'yan uwantakar gari ba, ba 'yan uwantakar ƙabila
ba. Allah yana cewa,
(Dukkan muminai 'yan uwan juna ne, ku sulhunta ‘yan
uwanku, ku ji tsoron Allah ko a ji ƙan
ku). [Hujurat: 10]
Dukkan
dangin alherin da kake so wa kanka, haka ake so ka so wa kowane ɗaya
daga cikin ɗaiɗaikun
al'ummar musulmai; dukkan sharri da ba ka so wa kanka, to irinsa ake so ka guje
wa dukkan ɗaiɗaikun
al'ummar musulmai.
No comments:
Post a Comment