GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Sep 14, 2011

ARBA'UNA HADITH (10) HADISI NA GOMA

An karɓo daga Abu Hurairata (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Lallai Allah tsarkakakke ne, kuma ba ya karɓar abu, sai tsarkakakke. Allah ya umarci muminai da irin abin da ya umarci Manzanni da shi. Ya ce, "Ya ku Manzanni! Ku ci daga daɗaɗan abubuwa, kuma ku yi aiki na-gari" kuma (Allah) ya faɗa (lokacin da yake umartar muminai) "Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ci daga daɗaɗan abubuwan da muka azurta ku da shi." Sannan (Annabi ) ya ambaci wani mutum, da yake tsawaita tafiya, gashin kansa ya yi gizo, ya yi ƙura, yana miƙa hannayensa zuwa ga sama, yana ccwa, "Ya Rabbi! Ya Rabbi!” amma kuma abincinsa haramun ne, abin shansa haramun ne, tufafmsa haramun ne, an ciyar da shi haram. Ta yaya za a amsa masa (addu'arsa)? (Muslim #1015)
                      
SHARH

Abin da ake nufi da, “....Allah Ta‘ala tsarkakakke ne...." shi ne kamili ne shi cikin siffofinsa, babu tawaya ko nakasa tare da shi (). Dukkan wani dangi na tawaya, Allah ya tsarkaka daga barinsa, dukkan dangi na kamala, Allah ya siffanta da wannan. Dukkan siffar da ke nuna kamala, to Allah shi ne da mafi cikar wannan siffar: Ilimi kamala ne, to Allah shi ya fi kowa ilimi; ƙarfi kamala ne, to Allah ya fi kowa ƙarfi, adalci kamala ne, to Allah shi ya fi kowa adalci a bayan ƙasa.

Dangane da faɗin Manzon Allah () cewa, "....kuma ba ya karɓar abu, sai tsarkakakke....", idan an ce aiki tsarkakakke, to ana nufin abin da ya cika sharuɗɗa waɗanda shari'a da gindaya a kansa, aikin da aka dogara da Alƙur'ani da hadisi dangane da tabbatuwarsa.
Dangane kuwa da faɗinsa cewa, "....Allah ya umarci muminai da irin abin da ya umarci Manzanni da shi....", a nan wurin, ka ga Allah ya ce wa Manzanni, "Ku ci daga daɗaɗan abubuwa...." ya ce kuma da muminai, "Ku ci daga daɗaɗan abubuwan da muka azurta ku da shi." Irin abin da Allah ya kallafa wa Manzanni, ya ce lallai su yi, haka ya ɗora wa bayinsa muminai. Wannan yana nuna mana, dukkan abin da mutum zai yi Allah ya karɓa, to ya zamanto wannan abin tsarkakakke, halatacce ne, ya cika sharuɗɗan da shari'a take buƙata. Kowace irin ibada, sai ta cika wannan! Idan ibada za a yi ta da dukiya, to ya zamanto dukiyar da aka yi wannan ibada da ita, dukiya ce ta halal, ba dukiya ce da aka same ta ta hanyar maguɗi ba. In za ka yi masallaci, in za ka yi makaranta, in za ka je hajji ko umara, ko za ka biya wa wani ya je, to ya zamanto dukiya ce ta halal, da guminka ka samu; ta hanyar .. fatauci, ko ta hanyar kasuwanci, ko mutuwa aka yi aka bar ta a gidanku, sai ka sarrafa ta wannan tasarrufin, to wannan ya halatta, kuma kana da lada a kai. Amma in dukiya ta kasance ta “maguɗi ko haram ce, ko ta ƙwace ce, ko ta sata ce, ko ta sama dafaɗi ka same ta, to ko ka bayar da kujera ɗari ko miliyan, ba ka da lada a wajen Allah. Ko ka ɗauki kuɗin sata ka je hajji, ko ka je umara, ba za a karɓa maka ba, domin "....Allah tsarkakakke ne, ba ya kuma karɓar abu, sai tsarkakakke...." Saboda haka wajibi ne mutum ya nemi halak cikin dukkan abin da zai yi, sannan ya bayar da dukiya ta halal. Haka kuma, ta iya yiwuwa abin naka na halal ne, sai dai ba ya da nagarta, sai ka ɗauka ka bayar sadaƙa, to Allah ba ya son irin wannan sadaƙar. Kamar abinci ya lalace, sai ka ɗauka ka bayar sadaƙa, ko ka taskance shinkafa ko masara ko gero a suto, har ya fara lalacewa, ta yadda ko ka kai shi kasuwa ba zai yi ƙima ba, ba zai yi daraja ba, wannan Allah ba zai saurare ka ba, saboda Allah Ta'ala mai tsarki ne, kuma ba ya karɓar aiki sai mai tsarki. Kuma Allah yana ccwa,

(Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ciyar daga daɗaɗan abubuwan da kuka tsururuta, da abin da muka fitar muku daga cikin ƙasa, kada ku nufaci lalatacce ku ce daga shi za ku ciyar, alhali ku ba za ku kabe shi ba, sai kun runtse idanu. Ku sani haƙiƙa Allah mawadaci ne abin godiya). [Bakara: 267]

Sannan Annabi () ya ambaci wani mutum da yake tsawaita tafiya: Wasu malamai sun ce tafiyar aikin hajji ce, wasu kuma sun ce tafiyar umara ce, wasu suka ce a'a! yana cikin tafiyar datake ta ɗa‘a ce. Ma'ana dai, wannan mutum yana cikin tafiya, kuma tafiyar ɗa'a ga Allah Ta‘ala, ga gashin kansa duk ya cure da juna, bai ma samu ya taje gashin kansa ba, duk ya ƙuƙƙulle saboda halin tafiya, sannan kuma, duk ya yi datti, ya yi ƙura. Manzon Allah () ya ambaci wannan mutum ya ce, "....yana miƙa hannayensa biyu biyu zuwa sama, yana cewa "Ya Rabbi! Ya Rabbi!!"amma kuma abincinsa haramun ne, abin shansa haramun ne, tufafinsa haramun ne, an ciyar da shi haram (tun yana yaro).
Ta yaya za a amsa masa (addu'arsa)?" Ma'ana, ai ba za a amsa masa ba. Sharaɗin da ake buƙata ga addu'a a yi ta, a karɓa, ya cika: Ga shi dai matafiyi ne, ana amsa addu'ar mutumin da yake matafiyi. Saboda haka lokacin tafiya, hali ne na amsa addu'ar mutum. Ga shi kuma, "....gashin kansa ya cakuɗe, ya yi ƙura...." wanda yake nuna yana cikin wahala. Duk mutumin da yake cikin halin tsanani, ana sa ran a karɓa masa addu’arsa, don Allah ya ce,

(Lallai a tare da tsanani akwai sauƙi. Lallai a tare da tsanani akwai wani sauƙi) [Sharahz5-6].

A nan wurin sauƙi biyu ne, tsanani ɗaya, waye zai rinjayi wani? Mutumin da ke cikin tsanani, ana sa ran sauƙi zai zo masa da wuri. Sannan kuma shi wannan mutumin da Manzon Allah () yake magana a kansa, ya yi riƙo da wani ladabi cikin ladubban addu'a, shi ne mutum ya ɗaga hannayensa sama. Annabi () in yana addu'a, yana ɗaga hannayensa sama. Hadisai mutawaturai suka zo daga Annabi () cewa, idan Annabi ()  yana addu'a yana ɗaga hannu sama, in ya gama addu'a kuma saukewa yake, ba ya shafa wa a fuska. Ga shi kuma mutumin ya tabbatar wa Allah rububiyyarsa, bai haɗa Allah da kowa ba, don yana cewa, ”Ya Rabbi! Ya Rabbi?!" Wato yana tabbatar wa Allah rububiyyarsa, imani da cewa ba wanda zai cire shi daga wannan abun, sai Allah. Tsabar tauhidi duk ya kankama, amma me ya kawo cikas aka ƙi karɓar addu'arsa? Abin da ya biyo baya shi ne, cewa, "....abincinsa haramun ne, abin shansa haramun ne, tufafinsa haramun ne, an ciyar da shi haram, ta yaya za a amsa masa (addu'arsa)?" Ba wai don addu'ar ce bai karanta daidai ba, ya karanta daidai; ba wai don bai ɗaga hannu ba, ya ɗaga hannu; ba wai don bai cancanta ba, ya cancanta, tunda yana cikin tsanani, amma me ya kawo masa cikas? Sharuɗɗai sun cika, amma sai aka samu wani abu da ke hanawa. Kamar mutum ne ya cancanci cin gado ta kowacce fuska, sai wani abu ya zo ya hana shi cin gado: Misali akwai dangantaka tsakaninsa da mamaci, kuma lallai mamacin ya mutu wannan yana da rai, ka ga dukkan sharuɗɗai da ake buƙata sun cika, wannan musulmi ne, wannan musulmi ne, sai muka bincika sai muka ga wannan ɗan, shi ya kashe mahaifinsa, ka ga ba za mu ba shi gado ba, tunda shi ya kashe mahaifinsa. Wannan hadisin yana nuna mana yunƙurin neman halal a cikin dukkanin al’amura: In za mu yi tufafi, ya zamanto halal ne, haka in za mu ci, ya zamanto halal ne, domin duk inda haramun take, ba ta da albarka, halal ita ce mai albarka, halal za ka ci ka kwanta lafiya, haram kuwa idan ka ci, ko ba ta tashi a nan ba, to za ta tashi a can. Saboda haka ya kamata mutum ya kiyaye wannan. Allah yana cewa;
 (Ka ce, "Halal da haram ba su zama ɗaya ba, ko da yawan harmun ɗin nan ya burge ka."). [Al Ma‘ida: 100].

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...