GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Oct 10, 2021

KITABUT-TAUHID (BABI NA GOMA SHA DAYA 11)

Ba A Yanka Domin Allah A Wani Wuri Da Aka Keɓance

Don Yanka Domin Waninsa(¹)

_____________________

SHARHI

(¹)Wannan babin zai yi magana a kan yanka ta ibada, wadda ba ta halatta a wajen da ake yanka don wanin Allah. Misali wajen da mushirikai suke yanka don neman kusanci da gunkinsu, ba ya halatta kai musulmi ka yanka ko da ragon layya ne a wajen! Ragon layya, ragon suna, ko hadaya duk waɗannan ana yin su ne domin Allah. Amma ba ya halatta ka yi waɗannan yankan a wajen da mushirakai suke yin yanka, duk da cewa kai abin da za ka yi ɗa'a ne.

**************************************************

 

Da faɗin Allah,

"Kada ka tsaya a cikinsa (masallaci) har abada…”

(2) (At-Tauba: 107-108)

__________________

SHARHI

 (²)Laa taƙum fihi abadan: Wannan aya na hani ga Annabi (SAW), yin sallah a wani masallaci da munafukai

suka gina, mai suna "Masjidu al-Dhirar, kamar yadda ya shahara a wurin malaman tafsiri da malaman tarihi.

Waɗanda suka gina masallacin, sun gina shi ne ba don neman kusanci ga Allah ba, sun gina shi ne don su riƙa haɗuwa su kawowa musulunci cikas, ko su gayyaci Annabi (SAW)masallacin, su far masa don su kashe shi. Shi ne Allah ya ce;

"Su ne waɗanda suka riƙi masallaci don cutarwa, don su bijire wa Allah da yunkurin raba kan musulmi; don su mayar da masallacin wata cibiya ga dukkan mai gaba da Allah da Manzonsa; za ka ji suna rantsuwa cewar babu abin da suka nufata sai aiki nagari. Allah ya san ƙarya suke yi. Kada ka tsaya a cikinsa (masallaci) har abada. Lallai masallacin da aka aza harsashinsa a kan taƙawa tun ranar farko, shi ne ya fi cancanta ka tsaya ka yi ibada a cikinsa. A cikinsa akwai mazaje da suke tsarkakewa, Allah yana son masu tsarkakewa." (At-Tauba: 107-108) Don haka, idan ya kasance masallaci ne, kuma manufar da aka gina shi ta tashi daga manufar da aka sani, ta koma irin waccan guda huɗu da ayar ta lissafa:

 a. Rikar masallaci don cutarwa.

b. Bijire wa Allah.

c. Yunƙurin raba kan musulmi.

d. Mayar da masallacin wata cibiya ga dukkan mai gaba da Allah da Manzonsa. Sai aka hana Annabi ( tsayawa ya yi ibada. To tun da sallah ma an hana ka yi ta a wurin da aka gina ba don Allah ba, haka ma yanka ibada ne, ba ya halatta ka yi shi a wurin da ake yin yanka ba don Allah ba.

Wannan shi ne alaƙa tsakanin ayar da matashiyar maganar. A nan wajen za ka gane fiƙhun Sheikh Muhammad ibn Abdulwahab, ya ƙulla babi, kuma ya kawo aya da take da alaƙa da babin.

*************************************************

 

An karɓo hadisi daga Thabit ibn Dhahhak (RA) ya ce,"Wani mutum ya taba yin bakance zai yanka raƙuminsa a wani wuri da ake kira Buwana, (wuri ne da yake kusa da Makka). Sai ya tambayi Manzon Allah (SAW) a kan haka. Sai Annabi ya ce, "Shin akwai wani

gunki na mutanen jahiliyya da ake bauta wa a wurin? Sai sahabbai suka ce, "A'a! Babu." Sai ya ce, "Shin akwai wani Idi da mutanen jahiliyya suka saba yi a wurin?" Sai suka ce, "Babu!" Sai Annabi ya ce, "Tafi ka cika bakancenka. Lallai babu ciko ga dukkan bakancen

da aka yi shi, in dai akwai saɓon Allah, ko cikin abin da dan Adam bai mallake shi ba." Imam Abu Dawud [#3313] ne ya ruwaito shi, kuma sanadinsa ya kai sharaɗin Bukhari da Muslim.(1)

______________________

SHARHI

(1)Ibn Hajar ya inganta shi, haka Sheikh Nasiruddeen Albani [Duba Mishkatul Masabih #3437].

Wannan hadisin na nuna halaccin yankan raƙuma don Allah, amma kuma yin sa a wurin da ba ayi don Allah, bai halatta ba. Yanzu, ga shi wannan mutumin ya yi bakance, amma ya ce sai ya je gari kaza zai yanka, sai Annabi (SAW) yake bincikar menene ya sa sai ya je wannan garin, shin akwai wani gunki a wannan gari? Ka ga idan akwai, Manzon Allah (SAW) ba zai bar shi ba. Shin akwai wani idi ko bikin jahiliyya da ake yi a wannan gari? In dai akwai, Annabi ba zai bar shi ba. Mahallush-shahid a nan wurin shi ne dukkan wurin da ake yin saɓon Allah, ba ya halatta ka je wurin, ko da bauta wa Allah za ka yi.

Shi ne malamai suka faɗaɗa wannan, suka ce, yana daga cikin wannan ko kama da haka, yadda aka karhanta mana sallah lokacin hudowar rana da faɗuwarta. Annabi (ya ce, domin a wannan lokacin masu bauta wa rana suke faɗuwa su yi mata sujjada. Duk da cewar lokacin da muke faɗuwa Allah muke yi wa, amma sai aka hana mu.

Domin a zamanin, idan muka yi sujjada, za ta yi kamanceceniya da ta masu bautar rana, sai Annabi (SAW) ya karhanta mana yin sallah a wurin, duk da cewa sallah ibada ce. Wato kenan, wannan na nuna yanke alaƙa ta dukkan kamanceceniya tsakanin al'ummar musulmi da wadda ba ta musulmi ba. Domin al'ummar musulmi, al'umma ce mai cin gashin kanta, ba wadda take rataye da wata al'umma ba.

Sannan kuma, bakance ibada ce, kuma kamar yadda ma'anarsa take, shi ne mutum ya lazumtar wa kansa ibada wadda ba wajibi ba.

Bakance iri biyu ne: Mu'allak ko Ghair Mu'allak.

a. Mu'allak: Misali, kana da ɗan uwa a asibiti, ka ce, matuƙar wane ya warke daga cuta, na yi alkawari tsakanina da Allah, sai na yanka rago, na yi sadaka da shi. Ka ratayar da sadaƙar ragon da warakar ɗan uwanka. Ko matarka tana da juna biyu, ka ce, matuƙar matata ta haihu lafiya, na yi alƙawari tsakanina da Allah, sai na yi azumin kwana uku. Ka ratayar da azumtar kwana uku da saukar matarka lafiya. Ba wajibi ba ne a kanka, amma tana sauka lafiya, ya zama wajibi sai ka yi. Haka, daga ranar da ɗan uwanka ya tashi daga rashin lafiya, ya zama wajibi sai ka yanka rago. Irin wannan makruhine a kanka, amma in dai ka yi, sai ka cika.

b.Ghair Mu 'allak: Misali, kana zaune sai ka ce, "Na-ji-na-gani, zan yantar da bawana wane." "Na-ji-na-gani, zan yi azumin kwana uku." Ka lazimtar wa kanka ba tare da ka rataya shi da wani amfani da kake son samu a duniya ba. Irin wannan bakancen babu karhanci a ciki.

Cika bakancenka: Wannan umarni ne, kuma dukkan umarni in dai ya zamanto babu wata ƙarina tare da shi, a kan ɗauke shi a matsayin wajabci. Ba a cire shi daga wajabci zuwa wani abu daban, sai idan akwai ƙarina da ta hana wajabci. To a nan umarni ne na wajabci? Shin lallai ne mutumin sai ya cika bakancen a wannan wurin? Abu ne guda biyu, bakance kansa, da wurin da ya ce zai yi bakancen. Lokacin da ya yi tambaya a kan abu guda biyu ne: Yanka raƙuma da wurin da zai yanka.

To da Annabi ya tashi yin tambaya, bai yi a kan raƙuman ba, sai ya yi ta a kan wurin. Da ya gama gamsuwa da wurin da za a yanka, sai ya yi umarni a kan cewa, "Cika bakancenka." To wannan umarnin shin ya shafi har

raƙuman ne tare da wurin ko kuwa wurin kawai? Ka ga ya shafi duka biyun ne; idan muka kalli raƙuman, ya shafi wajabci ne, idan kuma muka kalli wurin, ya shafí halacci.

Ba a cika bakance, idan mutum ya yi bakancen zai saba wa Allan Haka kuma ba a cika bakance cikin abin da mutum bai mallake shi ba Kamar ka ce, "Idan wane ya warke, sai na 'yanta bawan wane sadaƙaTun da ba naka ba ne, bai zama bakance ba.

 

A Cikin Wannan Babi Akwai Mas'aloli Kamar Haka:

1. Tafsirin ayar, "Kada ka tsaya a cikinsa (masallacin) har abada"

2. Sabo yana yin tasiri a wurin da ake yin sa. Haka ɗa'a ma tana da

tasiri

3. Juyar da mas'ala mai rikici i zuwa ga mas'ala mabayyaniya don warware rikicin.( Wato abin da malam yake nufi a nan, shi ne, da ya ce ba a yanka wajen da ake bautar wanin Allah, wannan zai wahala a fahimta,

Amma da ya alaƙanta da hukuncin sallah, wato, La taƙum fihi abadaa... sai abin ya fito fili.)

4. Mai fatawa ya halatta ya yi tambaya ga wanda ya yi masa fatawa, idan ya buƙaci hakan. (Mun fahimci wannan, ta inda Annabi (SAW) ya tambayi wanda ya yi

bakance wasu bayanan kafin ya ba shi amsa).

5. Kebance wani gari ko wuri da bakance, wannan babu laifí a shari'a, matuƙar ba wurin sabo ba ne.

6. An hana cika bakance a wuri, matukar akwai gunki a wurin na jahiliyya ko da a lokacin babu shi

7. Hana yanka ko cika bakance a wurin da maguzawa suka saba yin biki ko idi ko da bayan gushewarsu.

8. Ba ya halatta mnutum ya cika bakancensa a irin wannan wuri na saɓo, domin bakancen saɓo ne.

9. Hani dangane da kamanceceniya da kafirai a cikin idinsu, ko da a zuci mutum bai yi nufin haka ba.

10.Ba a yin bakance cikin abin da ya kasance saɓo ne.

11.Ɗan Adam ba ya yin bakance cikin abin da ba mallakarsa ba ne.

 

 (FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN GARIGAYI SHEIK JA’AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).  (zamuci gaba Insha Allah)

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...