GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Oct 1, 2021

KITABUT-TAUHID (BABI NA GOMA 10)

                                              Yin Yanka Don Wanin Allah(1)

__________________

SHARHI

(1)Wannan babin zai magana ne a kan ayoyi da hadisai da suke magana a

kan yanka ba don Allah ba. Mutum ya yi yanka ba don Allah ba. To

menene hukuncin hakan? Malamai sukan yi babi irin wannan ba tare da

sun faɗi hukunci ba, ko haram ne, ko halal, ko shirka da sauransu, su

kyale ka, su dogarar da kai da nassin da zai biyo baya. Nassosin da za su

zo, za su nuna maka yanka haƙƙi ne na wa? Idan ya tabbata yanka haƙƙi

ne na Allah (SWA) shi kaɗai, to yin yankan don wanin Allah ya zama

shirka

kenan.

Yanka, iri biyu ne. Akwai yanka da nufin ibada, shi ne mutum ya

kwantar da dabba ya yanka ta, da niyyar neman kusanci da Allah (SWA).

Kamar layya, hadaya, yankan suna ko fidiya, to irin wannan ba a yi wa

kowa sai Allah. Idan wani ya yi irin wannan yankan ga wanin Allah, to ya

yi babbar shirka mai fitar da mutum daga musulunci. Wanin Allah ya

hada da Annabi, mala'ika, shehi, aljani, ko wanene mutukar ba Allah ba

ne. don Labarawa a da, sai su yi ta kiwon dabba, sai ta girma a ƙarshen

shekara su zo su yanka ta ga gunkinsu don neman kusanci da gunkin.

Wannan babbar shirka ce. Har yanzu ma cikin masu karrama waliyyai

akwai masu yin haka, dabbar ma ba a yanka ta sai an je daidai kabarin

waliyyin, don a nuna neman kusanci da waliyyin. Wannan ma babbar

shirka ce ƙarara don bauta ce ga wanin Allah.

Akwai kuma yanka na dabi'a, misali mutum ya yanka kaji, ko

dabba saboda baƙi da zai yi, wannan ba komai, zai sami lada ma na

girmama baƙo.

 

*************************************

 

Da faɗar Allah;

"Ka ce, "Lallai sallata, da yankana, da rayuwata da mutuwata na

Allah ne, shi kaɗai Ubangijin halittu, ba shi da abokin tarayya, da

haka aka umarce ni, kuma ni ne farkon musulmi."(Al-An'aam 162-163)

____________________________

SHARHI

Kul inna salati: As-salat tana da ma'ana guda biyu, ta farko addu'a, ta

biyu ibada. Shin sallah da ma'anar addu'a ake nufi ko ibada? Wato wata

sananniyar ibada, ana buɗe ta da kabbara kuma a rufe ta da sallama.

Saboda haka, duk inda aka samu ma'anoni guda biyu, to ana nufin ta

shari'a, domin ita ake gabatarwa sama da ta Larabci. Domin Annabi (SAW)

ya zo ne ya koyar da shari'a ba Larabci ba.

Wa nuskii: Ana nufin ibada. A shari'ance ana nufin yanka.

Sheikhul Islam Ibn Taimiyya a wannan ayar yake cewa, Ubangiji (SWA) ya

haɗa tsakanin manya-manyan ibadu biyu: Mafi girman ibadar gangar jiki

ita ce sallah, sannan kuma mafi girman ibada ta dukiya, ita ce yanka,

domin neman kusanci a wurin Allah (SWA). Amma wasu suka ce zakka ta fi,

Allah ne masani.

Wa mahyaya: Abin da zan gudanar a rayuwata.

Wa mamatii: Kuma abin da zan mutu a kai ina ta yi. Domin ibada

ana yin ta ne har iya rayuwa, ba a dainawa. Shi ya sa Allah (SWA) ya ce

Ka bautawa Ubangijinka har sai yaƙi ni (mutuwa) ya zo ma" (Hijr:99)

Lillahi Rabbil Aalamin: Ya zamanto na Allah ne Ubangijin halitta.

Wabizaalika umirtu: Da haka aka umarce ni. Ya zamanto ibada

gabadayanta ta Allah (SWA) ce. Wannan shi ne Ikhlasi.

Wa ana awwalul muslimina: Kuma ni ne farkon musulmi. Me ake

nufi da farkon musulmi? Ko dai wannan ta zama awwaliyyatul

zamaniyyah ko awwaliyatul ma 'ana wiyyah. Awwaliyatul zamaniyyah shi

ne ya zamanto kafín a samu kowane mutum, Annabi ne farkon musulmi.

Awwaliyatul Ma'anawiyyah, wato kafinsa an yi wasu Annabawa da

al'ummomi da Alkur'ani ya nuna, amma musuluncinsa shi ne ya fi cika da

batsewa. A nan ma'ana ta biyu ake nufi. Domin idan ka ɗauki ma'ana ta

farko, ta saɓa wa ayoyin Alkur'ani. Awwaliyyatul zamaniyya ya nuna

cewa kafin sa an yi wasu Annabawa da al'ummomi da Alkur'ani ya nuna.

Duk inda aka kawo kissa, sai an faɗa wa Annabi (SAW) cewa ba ka nan

sanda abin ya faru, domin a nuna cewa akwai mutane da aka yi kafinsa.

Saboda haka, Annabi ba shi ne farkon mutane ba. Maganar cewa Annabi

shi ne farkon halitta, wannan magana ce mara asali. Hadisin Baihaƙi da

ya nuna haka, hadisi ne mara asali kuma na ƙarya [Duba Silsilatus Sahiha

#458]. Amma hadisi ingantacce, shi ne farkon halitta shi ne alkalami.

Allah ya ce da alƙalamil, "Rubuta duk abin da zai faru a duniya." [Duba

Sahih A-Jami 'us Sagir hadisi #3780] Hakan ya faru tun kafin a halicci

sama da ƙasa da shekara dubu hamsin (50,000) kamar yadda Annabi (SAW)

ya faɗa. Wannan ya nuna cewa ba shi ne farkon halitta ba. Kuma don an

ce ba Annabi (SAW) ba ne farkon halitta, ba ya nuna ba ka yabe shi ba. Allah

ya yi masa baiwa ba adadi wanda ba sai an ƙrƙiro ƙarya an jingina masa

ba sannan za a nuna fifikon Annabi (SAW). Allah ya sa mu gane.

********************************

Da faɗin Allah;

"Ka yi sallah domin Ubangijinka, kuma ka yi yanka domin

Ubangijinka."" (Al-Kauthar 2)

_____________________

SHARHI

Ayar farko da ta biyu, an nuna sallah da yanka haƙƙi ne na Allah (SWA).

Daga waɗannan ayoyi, za mu fahimci cewa domin Allah ne kaɗai ake

yanka, kishiyar haka kuma shirka ce mai fitar da mutum daga musulunci,

kamar masu yin yanka don aljani da kuma bokaye. Wanda galibi da

lokacin siyasa za ka ga ana ta yanka saboda aljani ko boka, don neman

biyan buƙatar 'yan siyasar da ba ruwan su da Allah. Ka ga ana ta yanka

jaki, da dabbobi, har ma mutane manya da yara, da jarirai. Ka ji ana ta

cigiya a filin sanarwa, amma ba a ga mutum ba, an yanka shi. Wannan

duk bauta ce ga aljanin da ya shar' anta yanka. Sai ka ga mutum ya aikata

haka, ya ci dan majalisa, ko gwamna, amma ya fita daga musulunci!

 

******************

An karɓo hadisi daga Aliyu ibn Abi Ɗalib ya ce, "Manzon

Allah (SAW) ya yi mini magana da kalmomi guda huɗu, "Allah ya

la'anci wanda ya yi yanka domin wanin Allah; Allah ya la'anci

wanda ya zagi mahaifansa biyu; Allah ya la'anci wanda ya ba da

kariya ga mai ɓarna; Allah ya la'anci wanda ya canza iyakoki

ƙasa." Muslim [#1978] ne ya ruwaito.

_____________________

SHARHI

Aliyu ibn Abi Dalib (RA), ɗaya daga cikin Khulafa'ur rashidun, ɗaya

daga cikin Al-ashratul-mubassharuna bil Jannah, kuma farkon wanda ya

musulunta cikin yara kanana, sirikin Annabi (SAW), mijin 'yarsa Faɗima

ya halarci yaƙiin Badar, yana cikin waɗanda suka halarci Bai'atur

Ridhwan kuma ya mutu shahidi, Abdurrahman ibn Muljim ne ya kashe

shi, a cikin watan Ramadan, shekara ta 40 bayan hijra.

Idan an ce la'anta, wato ana nufin korar mutum daga rahamar

Allah. Wato, Ubangiji ya nisantar da shi daga rahamarsa.

Allah ya la 'anci wanda ya yi yanka ba don Allah ba: Ya zamanto

ya yi domin neman kusanci a wurin wanin Allah; ya kasance mutum ne,

aljan ne, mala'ika ne ko ma dai wanene. Shin wanne ne ya fi girman laifi

tsakanin mutumin da ya yi nufin ya yi yanka, a zuciyarsa ba ya nufin

Allah, amma a wajen yanka sai ya ce, Bismillahi' da mutumin da ya yi

nufin yanka a zuciyarsa yana nufin Allah, amma a wajen yanka ya ce,

Bismil-Lat, ko Bismi-Manat' ko Bismi-Uzza?' Na farko dai shirka ya

yi, duk da ya ambaci Allah. Abin da ya yanka, daidai yake da abin da aka

yanka don wanin Allah. Ambatar sunan Allah da ya yi, ba ya kare

wancan. Na biyun kuwa sabo ya yi, yana da laifi, amma bai kai wancan

ba. Amma kuma wanda ya yi yanka domin ya girmama wani da nama,

amma a zuciyarsa ba da nufin ibada ba, don ya ciyar da mutane, wannan

ba zai shiga nan ba, domin da niyyar ihsani ya yi kuma zai samu lada

daidai niyyarsa. Abin da hukunci yake hararowa tsakanin aikin zuci da na

harshe, shi ne maganar zuci, wato niyya.

Allah ya la 'anci wanda ya zagi mahaifansa biyu. Duk lokacin da

aka ce mahaifi, kaka yana ɗaukar mahaifi, kamar yadda kaka mace tana

ɗaukar mahaifiya. Zagin mahaifi da zagin kaka, duk yana shiga cikin

wannan ma'anar. Haka zagin mahaifiya da zagin mahaifiyar uwa, shi ma

yana shiga ciki. Duk da cewa girman haƙƙi, yana tabbata ne ga abin da

yake uba na kai-tsaye, kafin kaka na ɗaya, biyu har na ƙarshe. Abin da

la anta take nufi a nan, zagi. Wato, lafazin la'ana' yana ɗaukar ma'ana

guda biyu: Korewa ga barin rahamar Ubangiji, da kuma zagi.

La'antar da aka jingina wa Allah, la'anta ce ta kore mutum daga

rahamar Allah. Sannan la'antar da ake jingina wa mutum na ɗaukar zagi

ko addu'a da la'anta. Annabi (SAW)ya fayyace abin a sarari cikin hadisi, da

ya ce, yana daga cikin manyan kaba'ira mutum, ya zagi mahaifansa. Sai

sahabbai suka ce, "Ta yaya mutum zai zagi mahaifansa? Sai Annabi ya

ce, "Kamar mutum ne ya zagi mahaifan wani, sai wancan ya rama a kan

mahaifansa." [Bukhari #5973] To ka ga, ba ya halatta yawan zagi.

Allah ya la 'anci wanda ya ba da kariya ga mai ɓarna: AI-Ihdathu

fiddeen, shi ne ƙirƙiro wani abu cikin addinin musulunci. Don haka, mai

bidi'a ake kiransa muhdith. Ko ya zamanto 'muhdith, mutumin da

yake kawo fasadi a cikin ƙasa. Misali, mutum ne yake sayar da barasa, sai

ka ba shi gidan haya; mace ce take zaman banza, sai ka ba ta gidan haya;

mutum ne ya saci kuɗin banki, sai ka je ka tsaya, ka karɓe shi beli. Ka ga

abin da ka yi, ka taimaki mai ɓarna, ko dai mai ɓarna ta fuskar addini, ka

taimake shi wajen yada bidi'a ko kuma mai ɓarna ta fuskar fasadi a cikin

ƙasa, ya ƙirƙiro zunubi, ya sanya mutane su rinƙa yi, ko yana sayar da

barasa, kwaya ko miyagun kwayoyi, ka ba shi mafaka, to la'anta ta hau

kanka. Laifi ne mai girma taimaka wa bidi'a, don shaiɗan ya fi son bidi'a

fiye da aikin saɓo, kamar yadda Sufyan ibn Uyainah ya ce, "Iblis ya fi son

bidi'a sama da aikin saɓo. Saboda galibin aikin saɓo ana tuba, amma

bidi'a kuwa ba a tuba." Domin mai aikin saɓo, ba zai yi inda za a gan shi

ba, amma mai yin bidi'a kuwa, sai ya shiga masallaci zai yi, har sai ya yi

mata alwala wani lokacin." Yanzu waye ake sa ran tuba tsakanin mai

bidi'a da mai saɓo? Shi mai saɓo ya san cewa laifi yake yi, don haka,

yana sa ran zai tuba. Amma kuwa mai bidi'a, shi gani yake yi ibada yake,

yana ganin abin da yake yi ɗin nan mai kyau ne.

Shi mai bidi'a, takara yake da Annabi (SAW), don Annabi zai cewa

mutane, "ku yi sallar walaha akwai lada, raka'atanil fajr ta fi duniya da

abin da yake cikinta, shafa'i da wuturi akwai lada,'wanda ya yi raka'a 12

a yini, na lamince masa shiga aljanna, biyu kafin Azzahar, huđu bayanta,

biyu bayan Magariba, biyu bayan Isha', sai raka 'atanil fajr." Da sauran

ayyuka kamar su salati da hailala da sauransu. To shi ma ɗan bidi'a sai ya

koma gefe ya ƙirƙiro nasa salatin daban, nasa tasbihin daban, nasa zikirin

daban, kuma ya ba su lada irin yadda Annabi ya ba wa nasa lada! Kai har

ma ya fi na Annabin lada! Shi ne Imam Malik ibn Anas yake cewa,

"Wanda duk ya ƙirƙiro bidi'a ya ce kyakkyawa ce, abin da yake nufi

Annabi ya ha'inci aikensa." Don Allah ya ce:

A yau na cika muku addininku.."(Maa'ida:3)

Sai wani ya z0 daga baya, bayan Annabi ya cika risala, kuma sai ya ce ga

wani salati, ko wuridi, ko wani abu kyakkyawa wanda Annabi bai gano

shi ba! Haka kuma ya ba wa ƙirƙirarren salatinsa sharaɗi sama da na

Annabin. Annabi yana ambaton Allah a kowane hali kamar yadda A isha

(RA) ta fada [Abu Dawud #18], ma'ana ko yana da alwala ko ba shi da ita.

Amma dan bidi'a sai ya kawo wani zikiri ko salati ya ce, "ba a yin sa sai

da tsarki na ruwa,' wato sai da alwala, ba a yi masa taimama! Shi ya sa

Allah ya la'anci mai taimakawa bidi'a, to ina ga me yin bidi'ar?!

Ya kamata mutum ya guji bidi'a, tun asalinta don kada ya faɗa

ciki. Duk abin da aka ce bidi'a ne, mutum ya yi ƙoƙarin kaucewa faɗawa

ciki.

Allah ya la 'anci wanda ya canza iyakokin ƙasa: Ma'ana mutum ya

canza iyakokin gonarsa da ta makwabcinsa, ko filinsa da na

makwabcinsa, ko iyakokin gidansa da na makwabcinsa. Duk mutumin da

ya yi wannan Allah ya la'ance shi. Misali an raba fulotai an ba wa kowa,

sai ka zo ka shiga cikin fulotin ɗan uwanka da taku ɗaya, to la'anta ta hau

kanka. To yanzu wanda ya ƙara iyaka ne ake magana a kansa, ina ga

wanda yake cinye wa mutane fulotai? Yanzu akwai mutanen da sun

shahara wajen cinye fulotan jama'a. Akwai wanda zai je ya sami filinka a

bayan gari, kawai ya je ya fara gini! Yaje ya sami ma'aikata maha'inta ya

yi bincike, a wane lokacin aka yanka filin, yaushe aka ba ka filin? Sai ya

sa a rubuta masa wata takardar da ya yi backdating din takardar, ya zamo

ya riga ka mallaka. Yanzu kai takardarka ko kimar takardar kosai ba ta da

ita! Shi wannan ya canza iyakar ƙasa, la'antar Allah ta hau shi. Shi kuma

ma'aikacin gwamnatin ya taimakawa mai ɓarna, shi ma ya shiga la'antar

jimlar baya.

Duk abin da za ka samu a rayuwa, na ƙwace filayen jama'a da

gidajensu, to yaushe ne shekarun da za ka zauna a gidajen? Sai ka ga

mutum ya mutu ya bar fuloti 40 ko 80, duk na wuru-wuru da cuku-cuku

da maguɗi, kuma yanzu hisabi yana jiransa gobe ƙiyama. Idan ka yi

wannan da, abin da zai sa a karɓi tubanka ba istigfari da hailala ba ne.

Wallahi idan kullum za ka yi istigfari miliyan, Ubangiji ba zai yafe maka

ba! Sai ka mayar da fulotin ga mai shi, ko kimar kuɗin fulotin ga mai shi,

idan ba ya nan, to ga magadansa, idan ba sa nan ga magaɗansu. Idan duk

ba ka san su ba, to ka ware kudɗn ka yi sadaka da su, Allah ya kai masa

ladan. Wallahi sai ka yi haka Allah zai yafe ma! Amma istigfarinka da

hailalarka, wallahi ba zai tsamar da kai gaban Allah (SWA) ba, kai da duk

waɗanda suka ɗaure ma gindi.

 

************************

An karbo hadisi daga Darik ibn Shihab ya ce, Manzon Allah

(SAW) ya ce, "Wani mutum zai shiga aljanna a sanadiyyar ƙuda, kuma

wani mutum zai shiga wuta a sanadiyyar ƙuda." Sai sahabbai suka

ce, "Yaya haka za ta faru, ya Ma'aikin Allah? Sai ya ce, ""Wasu

mutane guda biyu sun wuce inda wasu taron jama'a suke, suna da

wani gunki, ba sa barin kowa ya wuce ta wurin, sai mutum ya

gabatar da wani abu ga gunkin don neman kusancinsa. Sai suka ce

da ɗaya daga cikin waɗannan mutanen biyu ya gabatar da wani abu

ga gunkin nan. Sai ya ce, "Ba ni da komai da zan gabatar." Sai suka

ce da shi, "Ko da ƙuda ne (ka kashe ka gabatar)." Sai ya gabatar da

ƙuda, sannan suka buɗe masa hanya ya yi tafiyarsa." Sai Annabi ya

ce, "Don haka zai shiga wuta! Sai suka ce da ɗayan shi ma ya

gabatar da wani abu, sai ya ce "Babu yadda za a yi na gabatar da

wani abu ga wani ba Allah ba." Sai suka fille masa kai, sai ya shiga

aljanna!" Imam Ahmad ne ya ruwaito. [Cikin littafinsa Azzuhud

Shafi na 22]

_________________________

SHARHI

Darik ibn Shihab, wato Abu Abdullahi Al-Badali al-Ahmusiy. An yi

saɓanin kasancewarsa sahabi, amma galibin malamai sun ce sahabi ne, ya

ga Annabi, sai dai bai samu jin hadisi daga wurin Annabi ba. Ga shi ya

ruwaito hadisi daga Annabi (SAW), ya zama Mursal kenan. Amma ga ƙa'idar

malaman hadisi, Mursal ɗin hadisi daga wurin sahabi karɓaɓɓe ne a

zance mafi inganci. Ya ji hadisin ne daga wurin Salman al-Farisi, shi

kuma daga Annabi, duk da bai ambaci sunansa ba. Imam Ahmad ne ya

ruwaito shi a cikin Kitab al-Zuhud da kuma Abu Nu'aim a cikin littafin

Hilyatul Auliya' [J1/203). Kuma malamai sun yi saɓanin ingancinsa.

Waɗansu malaman suna sahihantar da shi, haka ma Sheikh Muhammad ibn Abdulwahab yake ɗaukarsa, don ya yi istinbaɗin hukunce-hukunce a ciki.

 

********************************************

A Cikin Wannan Babi Akwai Mas'aloli Kamar Haka:

1. Tafsirin ayar, Ƙul inna salati...

2. Tafsirin ayar, Fa salli lirabbika wanhar.

3. Farawa da la'antar wanda ya yi yanka ba don Allah ba.

4. La'antar wanda ya zagi mahaifansa. Yana shiga cikin wannan,

ka zagi iyayen mutum, shi ma ya zagi iyayenka.

5. La'antar wanda ya taimaki mai barna (ko dan bidi'a ko mai

sabo wajen aiwatar da sabonsa). Shi ne mutumin da zai farar

da wani abu wanda hakkin Allah ya zama wajibi a kansa, sai

ya fake da wani zai ba shi kariya don ya sarayar da haƙƙin

Allah a kansa.

6. La'antar mutumin da ya canza iyakar ƙasa. Shi ne iyakoki da

ake don su rarrabe iyakokinka da na makwabeinka; canza

iyakar shi ne jinkirtawa ko shigarwa.

7. Bambance tsakanin la'antar masu saɓo a jumlace da wani

mutum sananne guda ɗaya.

8. Wannan ƙissa mai girma, ita ce ƙissar ƙuda

9.Kasancewar wanda ya shiga wuta, zai shiga ne sanadiyyar

gabatar da abin da bai yi nufi da bauta ba, ya yi haka ne don

ya nisanci sharrinsu.

(A nan ne aka ci gyaran Sheikh Muhammad ibn Abdulwahab cewa, inda

a ce mutumin nan da ya yanka ƙuda a cikin zuciyarsa, bai yi nufin ibada

ba, amma ya yi don ya tsamar da kansa daga mutanen, wannan ba zai sa

ya rasa imaninsa ba. Domin ga ƙa'ida dukkan mutumin da ya aikata wani

abu don jin tsoron sharrin waɗansu, Ubangiji ba ya kama mutum da

wannan. Ubangiji ya ce "Wanda ya kafircewa Allah bayan imaninsa, sai dai wanda aka tilasta shi

alhalin zuciyarsa ta nutsu da imani, (wannan babu komai a kansa).

(Nah:106)

Wannan shi ne amanar ilimi, don Sheikh Muhammad ibn Abdulwahab ya

yi kuskure a nan to ba za mu bi shi ba. Sai mu roki Allah ya yafe masa, ba

ma yin taƙalidanci. Wannan ita ce da'awar sunna.)

10.Muminai sun gane girman shirka a zukatansu. Saboda yadda

wancan ya haƙura aka kashe shi, bai yarda ya goyi bayansu a

kan abin da suka nema ba, duk da cewa abin da suka nema

aiki ne na zahiri.

11. Wanda ya shiga wuta ɗin musulmi ne, domin da kafiri ne, to

da ba za a ce ya shiga wuta saboda ƙuda ba.

12. A cikin wannan hadisi akwai shaida dangane da wani hadisi

ingantacce da Annabi yake cewa, "Aljanna tana kusa da

ɗayanku sama da hancin takalminsa. Haka wuta ma." [Duba

Sahih Ibn Hibban #661]

13. Gane cewa aikin zuci shi ne babbar manufa, har a wurin

masu bautar gumaka.



(FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN GARIGAYI SHEIK JA’AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).  (zamuci gaba Insha Allah)

 

 

1 comment:

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...