GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Apr 20, 2020

KITABUT-TAUHID (BABI NA SHIDA 6)


Fassarar Tauhidi Da Kuma Kalmar Shahada

Da faɗar Allah;
"Waɗancan Waɗanda (masu shirka) suke roƙon su, su da kansu suna neman kusanci i zuwa ga (Allah) Ubangijinsu, don haka wanene a cikinsu ya fi kusanci i zuwa saduwa da yardar Allah." (Al-Israa":57)

___________________________


SHARHI
Dangane da saukar wannan aya, Abdullah ibn Mas'ud (RA) yake cewa,
"Wata tawaga ce cikin mutane, sai suke bauta wa aljanu. Aljanu suna ba su umarni su bi don samun biyan buƙatunsu na duniya. Ana nan a haka lokaci mai tsawo, sai aljanun suka musulunta, kuma suka cigaba da ɓauta wa Allah. Su kuwa Waɗancan mutane, ba su farga ba, suka cigaba da bauta wa aljanun, su kuma aljanun suna bauta wa Allah. Shi ne Allah ya ce, "Ka ga Waɗancan Waɗanda mutane suke roƙon su, su neman abin da
zai sada su da Allah suke yi, don haka waye a cikinsu ya fi dacewa da gaskiya. Wanda ya roki halitta ɗan uwansa, ko kuwa wanda ya roƙi Allah? Kuma suna fatan dacewa da rahamar Allah, suna jin tsoron azabar Allah." Kamar yadda ya zo a cikin Sahihul Bukhari (#4715). Amma akwai ruwaya daga Abullahi ibn Abbas (RA) da yake cewa ta sauka ne a kan mutanen da suke bauta wa salihan bayi, kamar su Annabi Isa, Uzairu,
Nana Maryam da mala'iku. Amma Shekhul Islam ibn Taimiyya ya ce, "Ayar za ta gasgata a kan waɗannan ma da Waɗanda ba su ba." Duk wani wanda yake bautar wani salihin bawa, wanda shi salihin bawan yana bautar Allah, to wannan ayar ta gasgata a kansa. Ya kasance an yi ne a da ko a yanzu, ko zai zo nan gaba." Duk wani salihin bawa da za a ce wane salihin bawa ne ko waliyyi ne da me yake samun salahar ko walittakar Da bin Allah ne, da bin umarninsa, da jin tsoron Allah, da fatan samum rahamarsa ne. Wannan shi ne zai mayar da shi salihi ko waliyyi. Da zarar an samu tarihin wani bawa da zai ce shí ba ya jin tsoron Allah, ko ba ya jin tsoron azabarsa, aljannar ma ba ya so, yana bauta wa Allah ne don shi ne Allah, to wannan ba waliyyi ba ne, yanzu ƙoƙari ake ya zama musulmi kenan, domin akwai nau'i na zindiƙanci tattare da shi. Shi ne Ibnul Kayyim yake cewa, "Siffa uku ce ake so a wurin salihin bawa: (a) ƙololuwar ƙauna zuwa ga Allah (al-mahabba) (b) fatan samun rahama (c) jin tsoron Allah." Duk wannan ayar ta haɗa su. Ashe ayar na nuna mana cewa, aikin ɗa'a shi ne wasila ɗin kenan. Ka riƙi aiki nagari da imani, jihadi, a matsayin shi ne wasilarka da zai sada ka da rahamar Allah. Yayin da kake aikin kuma, kada ka dogara da shi, har yanzu kana nan baynal khaufi war-raja 'a (wato tsoro da sa rai). Duk ibada, sai an gina ta a kan wannan. Idan ya zamanto kana tsoron azabar ne kaɗai, ba ka fatan samun rahama, har yanzu ba ka zama bawa nagari ba. Domin ya zamanto kana ɗebe tsammani daga rahamar Allah, Allah (SWA) kuwa ya ce, "Kada ku ɗebe tsammani daga rahamar Allah." Rahamar Allah (SWA) tana da yalwa. Domin babu mai ɗebe tsammani sai kafirai. Faɗin rahamar Allah shi ne zai sa kada ka ɗebe tsammani Na gaba, dole ka ji tsoron azabar. Sa rai wajen rahamar, ba tare da tsoron azabar ba, laifi ne. Haka kuma tsoron azabar, ba tare da sa rai da rahamar ba, shi ma laifi ne. Dole sai an sami ɓangare biyun.
Menene dangantakar ayar da wannan babin? Shi ne malamai suka ce, "Tauhidi shi ne yarda da kaɗaituwar Allah shi kaɗai." Wannan yardarm abu ne na zuci da harshe zai furta, idan harshe ya furta, gaɓɓai suka gasgata ta hanyar aiki. Wannan aiki da za ka yi, shi ne yake tabbatar da tauhidi ɗin, wanda shi aka sa wa suna a cikin ayar wasila. Sannan kuma a waje ɗaya, yana ƙara nuna mana alamar tauhidi, shi ne riƙar wasila zuwa wurin Allah. Abin da za ka riƙe ya zama wasilarka zuwa wurin Allah, shi
ne ibada, ba ka riƙi gangar jikin wani mutum ba. Ibadarka da za ka yi, to wannan shi ne wasilarka ta dacewa da rahamar Ubangiji, amma riƙar gangar jikin wani mutum, ya zama kishiyar tauhidi. Domin lokacin da ka riƙi gangar jikin wani mutum wasilarka, za ka zo ka bauta masa ka ƙyale Allah. Wannan shi ne dangantakar ayar da babin.

********************
Da Faɗin Allah

"Ka tuna wa al'ummarka yayin da Ibrahim ya faɗa wa mahaifinsa da mutanensa cewa. "Lallai ni na kuɓuta daga dukkan dangin abin da kuke bautawa, sai wanda ya ƙirƙiri halittata." (Az Zukhruf 26-28)
______________
Sharhi

Wannan abin da Annabi Ibrahim (AS) ya fa ɗa, shi ne, barrantar duk wani abin bautawa da mutanensa suke yi. Lokacin wasu na bautawa taurari, wasu gumaka da sauransu. To shi ne Annabi Ibrahim ya yi fito na fito da su, ya ce duk ba zai bauta musu ba, sai dai wanda ya ƙirƙiri halittata, wato ya halicce ni ba tare da ya ga samfuri a wajen wani ba. Shin menene alaƙar tauhidi da wannan ayar ko tafsirin kalmar? Abin nan da Annabi Ibrahim ya faɗa shi ne, tafsirin kalmar shahaɗa. Domin Kalmar shahaɗa ɓangarori biyu gare ta.
a. Laa ilaaha- Nafyun: Wato korewa kenan. Wannan ya yi daidai da faɗin Annabi Ibrahim "Lallai ni na kuɓuta daga dukkan dangin abin da kuke bautawa.
b. llallaahu-Ithbatun: Wannan shi ne tabbatarwa, kuma shi ya yi
daidai da faɗinsa "sai wanda ya ƙirƙiri halittata.
Korewa ita kaɗai, ba ta mayar da mutum musulmi, sai ya haɗa guda biyun. Wannan shi ne tafsirin kalmar shahaɗa. Ashe wannan maganar ta Annabi Ibrahim kalmar shahaɗa ce ya faɗa, don haka ƙarshen ayoyin suka nuna cewa kalma ce mai wanzuwa a cikin zuriyarsa.

*******************

Da faɗinsa;
"(Yahudu da nasara) sun riƙi malamansu da masu ibadarsu a
matsayin abubuwan bauta," (ATauba 31)
_______________
Sharhi

Abin da zai ƙara fito da wannan fili, shi ne hadisin Tirmizi [#3095], wanda Adiy bin Hatim Aɗɗa'i, da can kirista ne kafin ya musulunta. Da ayar nan ta sauka, ya zo wurin Annabi (ﷺ) yake cewa, "Ayar nan ta cikin Suuratut Tauba ta tuhumce mu kan cewa mun riƙi malamanmu da masu ibadarmu ababen bauta ne mun kyale Allah." Ya ce, "Ko alama ba mu taba riyawa cewar ababen bauta ne gare mu ba. Ta yaya aya za ta zarge mu da abin da ba laifinmu ba?" Sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Yanzu malamanku ba sa halatta muku haram ku bi su?" Sai ya ce, "Eh! Da wannan kam." "Kuma ba sa haramta muku halal?" Sai ya ce, "Eh!" Sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Ai wannan kuma ita ce bautar gare su.
Ba wai sai ka durƙusa ka yi masa bauta ba. Daga lokacin da
malaminka ya halatta maka abin da ka sani a Ƙur'ani da hadisi karara sun haramta, ka ajiye wannan ka bi shi, ka bauta masa. Ya ce maka, "Ai babu komai, irinku babu wani abu idan ka yi." Wannan shi ne malamai suke kira shirka ta ɗa'a. Ubangiji ya halicce ka don ya umarce ka, ya hane ka, sai wani ya zo ya yi maka umarni da hani saɓanin abin da Allah ya umarce ka, ko ya hane ka, kuma ka yi masa biyayya saboda kana ganin ai malaminka ne, kuma ka san lallai umarnin ya saɓa wa Allah, to shi ma ka bauta masa, ka haɗa shi kishıya da Allah. Wannan shi ne ma'anar Kalmar shahaɗa. Idan za ka faɗi kalmar sau miliyan a rana sau miliyan da dare, yin wannan kaɗai ka warware kalmar shahaɗar. Saboda aikinka kishiyar abin da kake faɗa ne. Allah bai halicci kowa ba sai don ya bi umarninsa shi kaɗai Duk wanda ya yi umami ya saɓawa Allah, sai a ajiye masa
umarnin a ƙi bi. Shin yahudu da nasara ne suka riƙi malamansu da masu ibadarsu, ko kuwa sun raba ne? Yahudu, su ne suka riƙi malamansu abin bauta, nasara, su kuma sun riƙi masu ibadarsu (masu bautar cikinsu). Kuma wannan shi ne ya fi rinjaye a wurinsu. (Ƙarin bayanin ayar zai zo a babi
na 38]

********************

Da faɗinsa;

"Daga cikin mutane akwai Waɗanda suke riƙar wanin Allah
matsayin kishiyoyi ga Allah, za ka ga suna ƙaunarsu kamar yadda ake ƙaunar Allah." (Al-Bakara 165)
__________________

Sharhi

Andadan: Jam'i ne na niddu. Idan an ce al-niddu, an ce alshibhu, wato kama, ka kamanta abu ga Allah (SWA). Ba wai ana nufin kamanta shi da Allah wajen sifa ba, domin ba su ga Allah ba, bare su kamanta shi da wani ba. Abin da ake nufi shi ne kamanta Allah ta wajen haƙƙi, shi ma su ba shi wata dama ta Allah (SWA) shi kaɗai, shi ma su samu irinta su be shi, sun kamanta shi da Allah kenan,
Me ake nufi da cewa, "Suna ƙaunatar su kamar ƙaunar Allah Shi
ne malamai suka ce, su waɗannan da suke riƙar kishiyoyi ga Allah, suna son waɗannan kishiyoyi irin son da suke wa Allah. Ma'ana sai suka raba soyayyar, rabi suka ba wa waɗannan kishiyoyin, rabi suka ba wa Allah, suna son su daidai-wa-daida da Allah. Wannan ya zama shirka kenan, domin son Allah, shi ne ƙololuwa. Amma ka haɗa soyayyar Allah da ta wani, mala'ika ne, Annabi Isa ne, Nana Maryam ce, wani salihin bawa ne, duk wannan shirka ce wadda ake kira Shirkul Mahabbati Waɗansu malamai suka ce, abin da ake nufi shi ne, suna son kishiyoyi ga Allah, kamar irin son da muminai suke yi wa Allah. Muminai nagari suna son Allah, so na ƙololuwa, duk a yayin da suka samu wani abu, za su nuna
cewa Allah (SWA) ne ya ba su. Haka su ma suke yi wa kishiyoyi ga Allah. Ma'anar ayar guda biyu ce, ko dai ta farkon ko ta biyun. Sai dai ma'anar farko ta fi bayyana a ayar. Muminai suna son Allah ƙauna ta ƙololuwa shi kaɗai, ba sa yarda su haɗa shi da wani. Ina ne inda ayar take da alaƙa da matashiyar magana? Inda matashiyar take, shi ne yadda Allah (SWA) yake cewa, "Ƙololuwar ƙaunarsu tana tabbata ga Allah." Wannan shi ne yake tabbatar da ma'anar, laailaaha illallaahu. Malamai suka yi ƙarin bayanin cewa, ita ƙauna, akwai ta ɗabi’a, wadda galibi zargi ko yabo ba shi da alaƙa da ita. Misali, ɗan Adam yana son nau'i na abinci, gida, tufafi da sauransu. Wannan ƙauna ce wadda ibada ba ta da alaƙa da ita ta kai tsaye. Amma irin ƙaunar da ibada take shiga ciki, ita ce wadda za ta sa ka ji ba ka iya saɓa umarnin wanda kake ƙauna ɗin ta kowane hali. Wannan ba zai yiwu a yi wa wani irin wannan ƙauna ta ƙololuwa ba, sai Allah, ta yadda ƙaunar ce za ta sa ba za ka iya saɓa umarninsa ba. Biyayya ga wanin Allah; ya haramta wa mutum halal ko ya halatta masa haram, shi ne ake kira Shirkul-Da'a.
Wadda kuma za ka ƙaunaci wani irin yadda za a ƙaunaci Allah, wannan ita ce Shirkul Mahabbati. Dukkan waɗannan suna rushe tauhidi ne gabaɗaya. Duk wanda ya yi su, zai wayi gari ba a cikin musulunci ba.
Don haka daidaita Allah da wani wurin ƙauna, shirka ne. Kuma duk wanda za a ƙaunata, ya zamanto Allah ne ya umarci a ƙaunace shi. Idan ka ƙaunaci wani don Allah, ka so wani gari ko gida don Allah, duk yana cikin ƙaunar Allah (SWA), kuma za ka samu lada a kai. Ka so gari don Allah, wato ka fifita Makka sama da sauran garurruka a cikin zuciyarka sama da garin da aka haife ka saboda Allah ya fifita ta; ka fifita Maɗina da Masjidul Aƙsa don Allah ya fifita su. Ka so wasu zamunna, ka fifita kwanaki goman farko na Zhul Hijja; darare goman ƙarshe na Ramadan a kan sauran darare, ka fifita daren Lailatul-ƙadr a kan sauran darare, ka so bayin Allah muminai maza da mata, duk wannan yana cikin ƙaunar Allah.

****************


Ya zo cikin Sahihi [Muslim #23] daga Annabi (ﷺ) ya ce
"Wanda duk ya ce, "La ilaha illallah," kuma ya kafirce wa abinda ake bautawa ba Allah ba, jininsa da dukiyarsa sun haramta (a yaƙe shi ko a ribace dukiyarsa), kuma hisabinsa yana ga Allah Madaukakin Sarki." Bayanin wannan babi shi ne abin da zai biyo baya na babi-babi.
__________
Sharhi

Abin da wannan hadisi yake da alaƙa da matashiyar magana, ma'anar, laa ilaaha illallaahu shi ne ka yarda da bautar Allah shi kaɗai, kada ya zama kana bauta wa Allah a karan-kanka, amma zuciyarka ta yarda ko an bauta wa wanin Allah babu komai. To ba ka yi daidai ba. Lallai sai ka yarda da duk wata ibada da ake yi ba ta Allah ba, rusashshiya ce, kuma kana fatan rushewar ta, kuma kana bin hanyoyin da za ka rage mabiyanta, da dukiyarka, ko iliminka ko dabararka. Wannan shi ne, laa ilaaha illallaahun ka ta tabbata. Amma ka faɗi, laa ilaaha illallaahu sau miliyan, amma ka ce, a kyale 'yan mishan su gina coci, ku kuma ku gina masallaci!


Cikin Wannan Babi Akwai Mas'aloli Mafiya Girma Da Mafi
Muhimmanci. Su Ne:

1. Tafsirin tauhidi da ma'anar kalmar shahada, da bayaninta da
al'amura bayyanannu.
2. Daga ciki akwai ayar cikin Suuratul Israa', wanda wannan
ayar ta mayar da martani a kan mushrikai Waɗanda suke kira salihan bayi A cikin akwai abin da yake nuna cewa kiran
salihan bayi shi ma babbar shirka ce.
3. Haka kuma akwai ayar nan ta cikin Suuratul Bara'a (Tauba),
an bayyana mana cewa, lallai Ahlul kitab sun riƙi malamansu da
masu ibadarsu a matsayin ababen bauta suka kyale Allah. Kuma
ya bayyana a ciki cewa, ba a umarce su da su bauta wa komai
ba, sai Allah shi kaɗai, Tare da nuna mana cewar, tafsirin ayar
wanda babu rikitarwa a cikinsa, nuni ne dangane da yin ɗa'a ga
malamai ko wasu masu ibada cikin sabo, ba wai roƙon su aka yi
ba.
4. A ciki akwai faɗin Khalil (AS) ga kafirai da ya ce, "Ni na
barranta (kuɓuta) daga abin da kuke bauta wa, sai dai wanda ya
halicce ni. Ma’ana wannan bara'a da ya yi, da ƙauna da ya nuna, shi ne tafsirin 'Shahaɗatu anla'ilaha illallah' Sai (Allah) ya ce "Kuma (Ibrahim) ya sanya (ita wannan magana) kalma mai wanzuwa cikin zuriyarsa. "Sai ya togace Ubangijinsa abin bauta, Allah ya nuna
5. Mun fahimci tafsirin ayar Suuratul Baƙara wadda ta shafi
kafirai inda Allah ya ce a kansu, "Sun shiga wuta babu dama su
fita." Laifinsu suna son kishiyoyin da suke jingina wa Allah,
kamar yadda ake son Allah shi kaɗai. Ga shi suna son Allah so
mai tsanani, amma wannan bai sanya shigarsu cikin musulunci
ba, to yaya wanda yake son kishiyar Allah sama da Allah? To,
ina ga wanda ba ya son komai, sai kishiyar Allah, kuma ba ya
son Allah?
6. Daga ciki akwai faɗin Annabi (ﷺ), "Wanda ya ce, 'Laa ilaaha
Illaallaahu 'kuma ya kafirce wa wani abin bauta, ba Allah ba, an
haramta jininsa da dukiyarsa, kuma hisabinsa yana ga Allah."
Wannan yana cikin mafi girman abin da yake bayyana ma'anar
laa ilaaha illallaahu'. Domin shi Manzon Allah, bai sanya faɗar
kalmar ita kaɗai ba, ta zamanto za ta kiyaye mutum da jininsa da
dukiyarsa. Kai ko da ma a ce ka san ma'anarta, tare da furta lafazinta, kai har ma da iƙirari da hakan, da ma kasancewar mutum ba ya bauta wa kowa, sai Allah shi kaɗai, ba tare da abokin tarayya ba, wannan duka ba zai haramta dukiyarsa da jininsa ba, har sai ya kara a kan haka, da kafirce wa duk abin da ake bauta wa ba Allah ba. Idan har ya yi kokwanto, ko ya yi inda-inda, dukiyarsa ko jininsa ba su zama haramun ba. Ka yi mamakin girman wannan mas'ala da buwayarta, da wannan bayani irin yadda ya fito fili, da hujjar da aka yi bayani. Shin akwai abin da ya fi ta zama yankan hujja a kan duk wanda yake jayayya?!


(FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN GARIGAYI SHEIK JA’AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).  (zamuci gaba Insha Allah)

1 comment:

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...