GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Mar 20, 2013

KITABUT-TAUHID (SHIMFIƊA):

Tauhidi, shi ne ginshikin al’amari gabaɗaya. Domin tabbatar datauhidi ne Allah  ya saukar da Iittattafai, kuma ya turo da manzanni. Sallah, azumi, zakka, hajji, kyautatawa iyaye, kyautatawa makwabta da duk Waɗansu
ayyuka na ibada, ba sa ingantuwa sai idan an gina su a kan tauhidi. Inda mutum zai ciyar da dukiya fan taɓa sama, Ubangiji  ba zai karɓa ba idan ba shi da tauhidi.
Abdullahi ibn Jud’an, wani mutum ne mai karamci da ciyar da maƙwabta, a lokacin jahiliyya har ya mutu bai karfii musulunci ba. Aisha (RA) take tambayar Annabi (SAW) cewa abin da Abdullahi ibn Jud’an ya ciyar, ranar tashin ƙiyama zai tashi ya samu tsira? Annabi (SAW) ya nuna cewa, duk abin da ya ciyar ba zai amfane shi ba ranar tashin ƙiyama. [Duba Muslim #214]. Don haka a tauhidi ne ake gina kowane irin aiki. Duk ibadar da mutum zai yi, ya yi ta zikin' da salatin Annabi, ya yi ta hailala da istigfari, ya ciyar da miskinai, matuƙar ba shi da tauhidi wallahi, Ubangiji (SWA) ba zai karƙa ba!
Abin da yake nuna muhimmancin tauhidi shi ne, tauhidi ne kaɗai abin da duniya ta haɗu a kai, tun daga Annabi Adam (AS) har i zuwa kan 'Annabi Muhammad (SAW). Daga Annabi zuwa Wani Annabin akan sha bamban a yanayin ibada, tsakanin hukunce- hukuncen tsarki, alwala da na ganima. Duk annabawa babu Wanda aka halattawa ganima da taimama sai Annabi (SAW). Tsakanin Annabi Musa (AS) da Annabi Isa (AS) akan samu an haramta wani abu a can kuma wannan ya zo da halacci. Kamar yadda Annabi Isa (AS) ya fada:
{ ولأحل لكم بعض الذي حرم عليكم}
"Kuma zan rika halatta muku wani sashi da ya zama haram a kanku (a cikin Attaura, yanzu Injila ta zo da halacci).” (Aali-!mraan:50) Annabi Muhammad (SAW) da ya zo, sai aka ce don ya sauƙaƙe dukkan tsananin da ke cikin waɗancan biyun.
Amma tauhidi tun daga farkon Annabi, zuwa Karshe (ɗaya ne. Sallah, azumi, zakka suna iya bambanta amma tauhidi iri ɗaya ne.
{ولقد بعثنا في كل أمة رسولا أن اعبدوا الله واجتنبوا الطاغوت}
"Kuma hakika mun aiko a cikin kowace al’umma, manzo, cewa ku bauta wa Allah kuma ku nisanci ɗagutu."(An-Nal;36)
Kuma ya ce:
{وما أرسلنا من قبلك من رسول إلا نوحي إليه أنه لا إله إلا أنا فاعبدون}
"Ba mu taɓa turo wa ba kafinka, wani manzo face mun yi wahayi zuwa gare shi, cewa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai ni, don haka ku bauta mini.” (AI-Anbiyaa:25) Kowa da ya zo abin da ya sanarwa al’ummarsa kenan. Wannan a jumlace kenan. A rarrabe kuwa dalla-dalla ga shi nan;
{ ولقد أرسلنا نوحا إلى قومه إني لكم نذير مبين{25 }أن لا تعبدوا إلا الله }
"Hakika mun turo Nuhu zuwa ga mutanensa, “Lallai ni a gare ku, mai gargadi ne, Wanda yake mabayyani, Kada ku kuskura, ku bauta wa kowa, sai Allah shi kaɗai.”"(Huud: 25-26) Kowane Annabi haka ya tabbatar da Wannan da’awar. Abin da zai ja hankalinka, shi ne, a cikin Suuratul Anbiyaa inda aka zana sunayen annabawa, aka fara da Annabi Musa (AS) da Harun (AS):
{ولقد آتينا موسى وهارون الفرقان وضياء وذكرا للمتقين}
"Hakika mun bai wa Musa da Haruna Alfurƙan sannan haské da kuma tunatarwa ga masu takawa." (Al-Anbiyaa:48)                                                                                                                                                                   Da aka yi gaba kadan cikin kissar Annabi Ibrahim (AS) sai aka ce;
{قال أفتعبدون من دون الله ما لا ينفعكم شيئا ولا يضركم}
"Sai ya ce shin yanzu kwa rika bautawa koma-bayan Allah, irin abin da ba zai amfane ku da komai ba, kuma ba zai cutar da ku ba?" (Al-Anbiyaa:66)
Da aka gama ƙissarsa, a can karshe sai aka kawo Luɗ (AS) aka. raɓa shi:
{ونجيناه ولوطا إلى الأرض التي باركنا فيها للعالمين}
"Kuma muka tsamar da shi da Lud i zuwa ga kasa wadda muka yi rnata albarka a cikinta saboda talikai."(A1-Anbiyaa:7l)
Sai aka haɗa da:
{ووهبنا له إسحاق ويعقوب نافلة وكلا جعلنا صالحين}
"Kuma muka ba shi Is'haƙ da Yakub a rnatsayin nafila, kowane ɗaya mun sa shi ya zarno salihi." (Al-Anbiyaa72)
Da aka gama da wannan, sai aka kawo Annabi Nuh (AS):
{ونوحا إذ نادى من قبل فاستجبنا له فنجيناه وأهله من الكرب العظيم}
"Tuna wa mutanenka ƙissar Nuhu, lokacin da ya yi kira, tun da, saimuka amsa masa, sai muka tserar da shi da iyalansa daga bakin ciki mai girma." (Al-Anbiyaa:76) '
Da aka gama da wannan, sai Dawud (AS) da Sulaiman (AS):
{وداوود وسليمان إذ يحكمان في الحرث إذ نفشت فيه غنم القوم وكنا لحكمهم شاهدين}
"Tuna wa mutanenka ƙiissar Dawud da Sulaiman, yayin da suka yi hukunci su biyu dangane da amfanin gona, lokacin da dabbobin suka kiwace shi da daddare, kuma mun kasance masu shaida dangane da  hukuncinsu.” (Al-Anbiyaa:78)
Da aka gama da su sai aka kawo Annabi Ayyub (AS):
{وأيوب إذ نادى ربه أني مسني الضر وأنت أرحم الراحمين}
"Tuna wa mutanenka ƙissar Ayyub, lokacin da ya kirayi Ubangijinsa, "Cuta kam ta shafe ni, kai kuma kai ne mafi jin Kan duk masgjin kai."(AI-Anbiyaa:83)
Sannan aka kawo Isma’il (AS), Idris (AS), da Zhulkifl (AS):
{وإسماعيل وإدريس وذا الكفل كل من الصابرين }
“Kuma Isma’il da Idris, da Zhulkifl, kowane ɗaya yana daga cikin masu hakuri.” (Al-Anbiyaa:85)
An gama da Wannan, sai Zannun (ma’abocin kifi), shi ne Annabi Yunus (AS):
{وذا النون إذ ذهب مغاضبا}
"Da kuma ma’abocin kifi lokacin da ya tafi yana mai fushi." (Al-Anbiyaa:87)
Daga nan sai Zakariyya (AS) da Yahya (AS):
 {وزكريا إذ نادى ربه رب لا تذرني فردا وأنت خير الوارثين}
"Da kuma Zakariyy, Iokacin da ya kira Ubangijinsa, "Ya Ubangiji! Kada ka bar ni tilo, kai ne fiyayyen masu gadarwa, "(A1-Anbiyaa:89) Sai aka kawo Annabi Isa (AS) ta hanyar izina.
Duk da aka gama sai aka cc:
{إن هذه أمتكم أمة واحدة وأنا ربكم فاعبدون}
"Lallai wannan, al’ummarku ce, al’umma guda ɗaya, kuma ni ne Ubangijinku, don haka ku bauta mini (Al-Anbiyaa:92)
Manufarsu duk guda ɗaya ce. Don haka da’awar annabawa duka a kan tauhidi take. Shi ne abin da idan ya gyaru sauran ayyuka sun gyaru. Idan ya rushe sauran ayyuka sun rushe. Shi ya sa koyar da tauhidi ya zama wajibi.
A Kur’ani an fara kira da tauhidi, aka saukar da wasu surorin da babu komai a cikinsu sai tauhidi. Aka yi shekara goma sha uku (13) a Makka babu abin da ake kira sai abu guda biyu, tauhidi da akhlaƙ. Sai sallah da aka shar’anta a daren Isra'I, amma sauran hukunce- hukunce sai da aka zo Madina. Abu na ƙarshe da ya sauka, Wajen tabbatar da tauhidi ne:
{واتقوا يوما ترجعون فيه إلى الله ثم توفى كل نفس ما كسبت وهم لا يظلمون}
"Kuma ku tsoraci wani yini da za a mayar da ku zuwa ga Allah a cikinsa, sannan kowace rai, a cika mata abin da ta aiwatar na aiki, su ba za a zalunce su kornai ba."(Al-Baƙara:281)
Karshen ayar da ta sauka kenan cikin AIkur’ani. An fara da tauhidi an rufe da tauhidi!
Haka kuma, tauhidi shi ne abin da yake haɗa al'umma. Wallahi, duk yadda ka yi ka haɗa kan al'umma a kan wani abu daban, Wata ƙa’ida daban saɓanin tauhidi, ba za ka iya ba. Jam’iyyar siyasa ba za ta iya ba, Wani tsarin mulki (constitution) ba zai iya hada su ba. Wata dabara da za a yi wa aya, duk ba zai fitar da rnutane ba. Sai ka sa a zuciyar kowa ya ji ba ya jin girma ko kimar Wani abu sama da Allah (SWA) da Manzon Allah (SAW). Ba Wanda ya isa ya talauta Wani, ko ya cutar da shi, sai Allah (SWA). Sannan idan ni'ima ce, ba Wanda ya isa ya kawo ta, sai shi. Sai duk duniya ta yarda da haka, to sai kai ya haɗu. Idan kuwa duniya ba ta yarda da Wannan Ka’idar ba, kowa ya zaɓi Wanda yake ganin zai fisshe shi, to ba za a taɓa haɗuwa ba.
Misali, lokacln da aka turo Annabi (SAW) ya samu Larabawa, Kasa ta hada su, launin fata da yare ya haɗa su, suna magana da harshe ɗaya, amma ko da a cikin garin Makka, kowane dangi babu ruwansa da ɗayan. Aws da Khazraj a Madina, shekara arba’in suna yaki da juna, asalinsu guda daya ne, daga Yemen suka taso suka dawo Madina, a sakamakon rushewar farko ta Dam a tarihi, Wato Ma’arib. A cikin Suuratus Saba ’Allah ya ba da labarin. Babu Wanda ya sasanta su sai Annabi Muhammad (SAW) da ya kawo tauhidi.
Idan ka duba tarihin Larabawa babu abin da suka yi Wake a kai sai rigima. Babu Wanda bai yi Waka a kan faɗa ko rigima ba. Waƙoƙin, idan an tara gabadaya, a kan rigima ne. Idan ka ɗauki Waƙar Amru ibn Kulthum, shi ma rigima ne da faɗa, yana hakaito yaƙe-yaƙen da suka yi da sauran mutane. Ba su da Wani addini sai faɗa, giya, da neman mata. Amma addini ya zo gabaɗaya ya haɗa kansu.
Don haka Allah (SAW) ya tunasar da Annabi (SAW), ya ce da shi :
 {وألف بين قلوبهم لو أنفقت ما في الأرض جميعا ما ألفت بين قلوبهم ولكن الله ألف بينهم إنه عزيز حكيم}
"Kuma ya sanya soyayya a tsakanin zukatansu. Da za ka ciyar da abin da yake cikin ƙasa, gabaɗaya, da ba ka sanya soyayya a tsakanin zukatansu ba, amma kuma Allah ya sanya soyayya a tsakaninsu. Lallai shi mabuwayi ne mai hikima."(Anfal;63)
Don haka tauhidi shi zai gyara al'umma. Yau duniya tana bukatuwa i zuwa ga tauhidi irin bukatuwar da ta yi kafin turo Annabi (SAW). Domin a lokacin, duniya na cike da rigima. Farisawa da Rumawa a lokacin su ne duniya, suna faɗa da juna. Yahudu da nasara suna faɗa da juna. Larabawa a karan kansu suna faɗa da juna. Sai da Annabi (SAW) ya zo, Kur’ani ya sauka aka warware rikicin Makka, aka je Madina aka warware gaba ɗaya rikicin Madina. Haka kuma, aka warwarc rikicin ƙasashen (Gufl) gabas ta tsakiya. Daga nan sai musulunci ya sauka a kasar Sham (suna Karkashin daular Rumawa) aka gama da su, aka je har Rum. Sannan musulunci ya yi arewa ya kusa ya shiga Iraƙ, aka gama da nan, aka shiga aka karya daular Farisawa, sai da musulunci ya haɗe duniyar bakiɗaya. Shugabanci ɗaya take bi. Ba a taɓa samun haɗin kai a duniya ba irin wannan lokacin. Me ya kawo wannan haɗin kan? Wallafar wani ne? ko dabarar wani ce? A’a, tauhidi aka tsayar sai kan kowa ya haɗu.
Haka kuma, duniya yau ta shiga rikici sakamakon raunin tauhidi. Babu inda ba a fada; Afrika ta yamma, kudu, da ta tsakiya, rigima! Kasashen Larabawa rigima! Kwantacciya tsakanin Saudiya da Yemen, tsakanin kasashen Larabawa da Iran, yanzu kuma da lrak. Tsakanin Iran da Bahrain. Su kansu Turai ba su zauna lafiya ba. Tsakanin Croatia da Serbia rigima! Northem Ireland, ‘Cambodia, rigima! Tsakanin Korea ta Arewa da ta Kudu, rigima! India da Pakistan rigima! Ko’ina ana bala’i! Majalisar dinkin duniya tana nan, majalisar haɗin kan ƙasashen Afrika tana nan, kungiyar hadin kan Kasashe rainon Faransa da rainon Ingila suna nan, ƙungiyar hadin kan Larabawa tana nan, majalisar zartarwa ta kasashen (Gulf) gabas ta tsakiya tana nan. Dukkansu babu abin da suka tsinanawa duniya, kuma babu abin da za su tsinana. Babu abin da zai kawar da rikicin duniya sai tauhidi. Daga nan za ka gane muhimmancin
tauhidi.
Don haka, tauhidi yana bukatar karatu na nutsuwa don shi ne zai Warwarewa al’umma dukkan matsalolinsu, ya tabbatarwa da al’umma arzikin duniya da na lahira.


FASSARA DA SHARHI DAGA MARIGAYI SHEIK JAFAR MAHAMUD ADAM (RAHIMULLAH)

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...