GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Dec 24, 2014

KITABUT-TAUHID (BABI NA UKU 3)


Duk Wanda Ya Tabbatar Da Tauhidi Zai Shiga Aljanna Ba Tare Da Hisabi Ba
_______________
SHARHI;
Wannan babin kamar cukon babin baya ne. Babin baya ya yi bayani akan falalar tauhidi da yadda yake kankare zunubai. Wannan kuma zai yi bayanin cewa, duk wanda ya tabbatar da tauhidi, haƙiƙanin tauhidi, to zai shiga aljanna ba tare da hisabi ba, wato babu ƙididdugar ayyuka, kuma babu azaba. Ana tashi ƙiyama,
sai a kai su aljanna. Allah Ya sanya mu acikinsu. Amin       
            Haƙiƙani tauhidi shi ne, tace shi daga dukkan datti da shirka, wato mutum bai yadda da malamin duba ba, bai yadda da boka ba, dukkan wani abun da yake haƙƙin Allah (SWA) ne ya tabbatar masa Shi kaɗai. Sannan kuma ya tace tauhidi daga dukkan wani dangi na bidi’a ta faɗa a baka, ko a aiki.
To wannan kuma ba zai yiwu ba said a karatun yau da gobe. Domin ba yadda za ayi mutum ya san dukkan bidi’o’in da suke garinsu. Dole sai da karatu mutum zai ji wannan abu bidi’a ne sai ya daina. Yadda kullum kake nisantar bidi’a, haka tauhidinka yake ƙara haske, kana ƙara tace shi da wanke shi, har ka shiga cikin waɗanda suke tabbatar da tauhidi.

                                    **************************
Da faɗin Allah; “Lallai Ibrahim ya kasance jagora, mai ƙanƙan da kai ga Allah, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga masu shirka ba.”( An- Nahl:120)     
____________
SHARHI;
            Wannan ayar ta yi bayanin suffofi guda huɗu, wanda duk ya suffanta dasu, kamar yadda annabi Ibrahinm (ASW) ya suffanta dasu, to ya tabbatar da tauhidi, haƙiƙanin tabbatarwa.
Ummatun; Wato shugaba abin koyi. Ba ka zama shugaba abin koyi, sai ka tara dukkan suffofi abin yabo, ka nisaci dukkan siffofi ababen ƙi gwargwadon hali. A cikin ajin farko na alma’aruf, shi ne tauhidi, sannan ibada, kyawawan ɗabi’u, mu’amala da sauransu. A cikin munkari abin da ya fito a ajin farko, itace shirka, bidi’a da saɓo. Wanda duk ya suffantu da wɗannan halaye, to zai zamto Umma, wato abin koyi, a ban-ƙasa, ko da shi kaɗai ne. An rawaito daga Abdullahi ibn Abbas, ruwayar Ibnu Abi Hatim ya ce, “A lokacin annabi Ibrahim banda shi, babu kowa musilmi a ban-ƙasa, har sai lokacin da ya yi hijira suka haɗu da Annabi Luɗ (ASW), sannan Ubangiji Ya ba shi ‘ya ‘ya. Daga nan ne aka fara samun musulmi” [Duba Tafsirin Ibn Abu Hatim tafsirin suuratun Nuhl 9/127] Lokacin da aka kawo ƙissar za’a halaka Annabi Ibrahim, a sa shi a wuta shi kaɗai ne, ba a ce za a sa su tare da wani ba. Domin shi kaɗai ne musulmi kuma saƙon da aka aiko wa al’umma, suka ƙi karɓa, shi kaɗai ya karɓa, ya zama al’umma.
            Ƙanitan-lillahi: Sheikhul Islam ibn Taimiyya ya ce, ‘Alƙunut’ shi ne dimantar ɗa’a. Babu yadda za a ce ka dimanci ɗa’a awa ashitrin da huɗu, sai dai abin da ake nufi shine a sami kasha tamanin ko casa’in cikin ɗari. Annabi Ibrahim(ASW) kuwa zai iya samun kasha ɗari, domin shi ma’asumi ne kuma Annabi n. amma wanda ba Annabi ba, to ba zai iya dimantar ɗa’a ba. Sai daya ya zamanto alherinka ya yi yawa. Tunda ba zaka iya tsarkake kanka daga zunubi ba, to ka zamanto irin mutanen da idan sun yi zunub, ba sa dawwama a kai. Ya zamanto da ka yi zunubi, sai ka dimanci istigfari, sai ka samu  gafarar Ubangiji, ka dimanci ɗa’a, yawan sallar dare, istigfari da salatin Annabi.
            Hanifan: Ibnul Ƙayyim  y ace,  “Mutumin day a fuskanci Allah (SWA), kuma ya kawar da kai daga dukkan abin da ya zama dangin buƙata na irin wanda ɗan Adam ba ya iya ya, ka fuskanci  Allah das hi. Dukkan abin da yake haƙƙi ne na Allah, wato ibada kenan, kowace iri ce ka nufaci Allah (SWA) da ita, to idan ka yi haka, ka zama ‘hanif’, kuma haka ake so mutane su zama ‘hunafa’a’.
            Wa lam yaku minal mushrikin: Bai kasance da masu shirka ba. Me ake nufi da haka? Wato ba ya yin shirka, kuma bai goyi baya ba. Ko da ba  yin shirka, sai ya zamto ba ka goyi bayan a yi ba. Wannan rashin goyon bayan a yi, zai ɗauki mataki daban-daban. Wataƙila kana da ƙarfin da za ka hana, to sai ka hana ɗin, ko kana da ƙarfin da za ka iya hanawa da hannu, to ka yi hakan. Wataƙila ba ka da dama, sai dai ka ƙiabin a zuciya, sai ka yi ko kuma ka ta shi daga wurin ka koma inda ake tauhidi  tsantsa, ko mai jin daɗin da kake yi a wurin. Tauhidi bay a yiwuwa sai ka ƙi shirka, sai ka yi fito-na-fito da mai yin shirka. Kada ka ce zaka zauna da mutanan da suke shirka. Haka Annabi Ibrahim (ASW) ya yi da mutanensa da mahaifinsa ahalin da suka shiga na shirka. Ya yi musu wa’azi sukaƙi ji, sai ya yi hijira, sakamakon haka Allah (SWA) Ya saka masa da ‘ya ‘ya duka Annabawa, Isma’il da Is’haƙa. Don haka duk wanda ba zai sake wurin bautar Ubangiji ba, wajibi ne ya canza wuri. Idan unguwa ce ko gari ko ƙasa ce, ya canza wata. Don haka ba a yanke hijira ba, daga nan har ƙiyama,tana nan.
                                  
                                     ********************
            Da faɗinSa;    
 “(Bayina nagari) su ne waɗanda ba sa yin shirka da Ubangijinsu” (Al- Muminun:59)
________________
SHARHI;
       Asali shiraka iri biyu ce: Akwai babbar shirka (Shirkul Akbar); it ace take ɗaukar mutum daga musulunci, ta kai shi wajen musulunci. Wato, bautwa wanin Allah, ko ka roƙi wani, ka yi sallah ko azumi don wani, ka yi bakance saboda wani, irin abin da ake yi don Allah, amma sai ka yi don wani. Waɗannan duk nau’ika ne na shirka.                            
            Akwai shirka ƙarama (Shirkul Agar); misali riya, kamar yadda Manzon Allah (ﷺ)  ya fassara. Menene riya? Asalin abu ka yi shi don Allah, amma sai ka kyautata abin don wani ya yaba, ko da ba don wannan ba, ka iya yin aikin, amma ganinsa sai ka kyautata don ya ce ya yi, ko ka yi don ka munana wa wane, to wannan ya zamo ba don Allah ba tsantsa. Wannan shirk ace ƙarama. Ba ta mayar da mutum kafiri,sai dai dukkan aikin da irin wannan shirka ta shiga ya lalace, Allah ba zai karɓi wannan aiki ba, kamar yadda Allah ya ce, “Ni na wadata da a haɗa ni da abokin tarayya. Duk wanda ya aikata aiki, sai ya haɗa ni da wani, (yana son na ba shi lada, kuma yana son wane ya bas hi ), ni wadatacce ne, sai na bar wa wancan ɗin shi kaɗai,”[Muslim #2985,Ibn Majah #4202]. Wannan riya da take shiga cikin aiki, ta zama ƙaramar shirka, ko ta lalata aiki. Malamai suka ce yaushe ne za ta lalata aiki kuma yaushe ne ba za ta lalata ba? Don akwai bambancin riya da ta shiga daga farkon aiki har ta kai ƙarshe, akwai bambanci a kan riyar da ka yi zango a cikin aikin, ka yi rabi, sai wani ya gani, sai ka kyautata masa rabin. Farko, kana yi don Allah, amma a tsakiya sai wani ya ga kana yi, sai ka kyautata masa rabi. Duk malamai sun yi magana a kan wannan; Musamman Hafiz Ibn Hajar Askalani a cikin sharhin hadisin Innamal a'amaalu binniyat-wa Innama likullim-ri’im maanawa, a cikin Fathul Bari, [ƙarƙashin hadisi na ɗaya] Haka kuma, Imam Ibn Rajab al-Hambali a cikin sharhin da ya yi wa ‘Arba ’una Hadithan, [ƙarkashin hadisi na ɗaya] ya yi sharhi mai kyau a ciki. A taƙaice dai, riya ƙaramar shirka ce. [Don ƙarin bayani duba Fassara da Sharhin Arba’una Hadithan, na Sheikh Ja’afar Mahmoud Adam, ƙarƙashin hadisi na ɗaya.]

Haka kuma, rantsuwa da wanin Allah, amma ba ta fitar da mutum daga musulunci, kamar yadda malamai suka yi bayani. Domin wani ya zo ya rantse da Annabi da mala’ika Jibrilu, ya ce, “Na rantse da Annabi, na rantse da mala’ika J ibrilu, na rantse da kabarin Nana Fatima!” Ka ga ya yi shirka, amma ƙarama, bai fita daga musulunci ba. Musulmi ne amma yana ƙaramar shirka. Domin Manzon Allah ya ce, “Duk wanda yake son yin rantsuwa, to ya rantse da Allah, ko ya yi shiru.” [Bukhari #6108,627O Muslim #1646] lrin wannan shirkar daidai take da kaba'ira, babban laifin da akwai zunubi na nan tuli, har sai idan mutum ya tuba a kankare shi, ko idan yana da wani abin da zai sa a kankare zunubin cikin dangin abubuwa goma sha biyu da Ibnul Kayyim ya yi bayaninsu a cikin littafin, ‘Madarijus-Salikin bayna manazilu lyyaka na’abudu wa-Iyyaka nasta'in idan ba haka ba, za a kama shi da azaba.

Haka kuma, kuka na mutuwa ma shirka ce ƙarama. Haka dukkan kaba’ira a wurin wasu malaman, shirka ce ƙarama. Wasu suna cewa, ba za a ce dukkanninsu ba. sai idan Annabi (ﷺ)  ya tabbatar cewa shirka ne, ko ya sanya musu suna aI-kufur ko al-shirk, kuma muka ga cewa, bai kai al-shirkul-akbar ba, sai mu sa masa al-shirkul Asgar ko al-kufurul-Asgan Kamar yadda Annabi (ﷺ)  ya nuna cewa, kukan mutuwa irin wanda ake yi ana ambaton ayyukan mamaci, ya sanya masa suna kafirci. Haka kuma, alfahari da ƙabila ko da gari ko yare, su ma duk Annabi (ﷺ)  ya sa musu suna kafirci. To, amma duk ana sa su a cikin ƙaramin kafirci ko ƙaramar shirka.

To, tauhidi ba a tace shi, sai idan mutum ya nisanci Shirkul Akbar da shirkul Asgar, to zai shiga aljanna ba tare da hisabi da azaba ba. Wanda ya nisanci Shirkul akbar, amma yana Shirkul Asgar zai shiga aljanna, amma zai iya yiwuwa da hisabi. Don haka  Allah Y ace;
“Waɗanda ba sa shirka da Ubangijinsu” (Al-Muminun:59)
A takaice dai, ana kore dangin shirka ne, kowanne iri. Ana nufin muminai ba sa kowanne irin shirka babba da ƙarama. Kuma suna nisantar kaba’ira, sai dai wani lokaci su faɗa ciki su tuba.

********************
An karbo daga Husain ibn Abdurrahman, ya ce, “Na kasance a wurin Sa’id bin Jubair, sai ya ce, “Waye a cikinku wanda ya ga tauraron da ya faɗo da daddare?” Sai na ce da shi ‘ni’ Sai na ce, “Ku saurara! Ba fa sallah nake ba lokacin da na gan shi, sai dai kunama ce ta harbe ni.” Sai ya ce, “Me ka yi (da kunama ta harbe ka)?” Sai na ce, “Na yi tofi (ruƙya) ne.” Sai ya ce, “Wa ya ce ka yi tofi?” Sai na ce, “Wani hadisi ne da Sha’abiy ya faɗa mana.” Sai ya ce, “Me ya faɗa muku?” Sai na ce, “Ya ba mu hadisi daga Buraidata bin Husaib (Ibn Haris al-Aslamiy) ya ce, “Ba a yin tofi sai idan kambun baka ya samu mutum, ko wani abu mai dafi ya harbe ka da ƙarinsa.” Sai ya ce, “Duk wanda ya yi aiki da abin da ya ji, to ya kyauta.
____________
SHARHI;
Sa’id bin Jubair babban tabi’i ne, ɗaya daga cikin ɗaliban Abdullahi bin Abbas. Ya mutu shekara ta 59 bayan Hijira. Hajjaj bin Yusuf ne ya kashe shi don zalunci.
“Wa ya ce ka yi tofi?" Sai na ce, “Wani hadisi ne da Sha’abiy ya faɗa mana.” Wannan sai ya nuna duk abin da mutum zai yi a musulunci sai yana da hujja ta shari’a. Sannan kuma, hujjar kowa shi ne, hadisin Annabi (ﷺ) . Ba a kafa hujja da cewa ‘malam wane ya ce...’ sai dai fadar Annabi (ﷺ) .
AI-Ain shi ne kambun-baka. Kambun-baka yadda yake kuwa, Ubungiji yana halittar wasu mutane da tasiri ko a idonsu ko a harshensu, ta yadda idan suka ga abu ya burge su, ko suka ƙawata abin da bakinsu, idan ya burge su, kawai sai abin ya faɗi. Galibi ba da niyya suke yi ba, wasu ma ba su san sun yi ba, sai daga baya a faɗakar da su. Wasu kuwa sukan gane sun yi. Dukkan wanda wani ya kalle shi, aka gane, kuma ya faɗi, sai a yi masa tofi. Mafi girman abin da za ka yi masa tofi da shi, shi ne Suuratul Faatiha.
Hanya ta biyu, hadisin da Imam Malik ya rawaito a cikin Muwaɗɗa, hadisi ne ingantacce na Sahl Bin Hunaif. Wani sahabi ya kwaɓe yana wanka, sai wani ɗan uwansa ya gan shi, sai ya ce, “Kai! Yau na ga wani mutum mai kyan fata." Kurum sai ya faɗi Aka ɗauko shi aka kawo shi wurin Annabi (ﷺ) . Annabi ya tambayi abin da ya faru. Suka ce, mun ji wane ya ce kaza, kawai sai muka ga ya faɗi. Sai Annabi ya ce, “Don me sashinku zai kashe sashi?" Sai ya ce, “Ya Annabin Allah! Babu abin da na yi, ga abin da na ce jikinsa ya burge ni, na ce, “Kai! Allah ya ba wa wane jiki mai kyau.” Sai Annabi (ﷺ)  ya ce, “Ina ma ka ce, ‘Barakallahu fi ka!”-Allah ya ba ka kyakkyawar fata. Da ka faɗi haka, da bai kamu ba. To zo ka yi alwala.” Sai ya yi alwala a kasko, amma bai zubar da ruwan ba, sai aka je aka yayyafa wa wannan mutumin, sai ya tashi [Muwadda #1679]. Wannan ita ce hanya ta biyu ta maganin kambun-baka. Hanya ta farko kafin faruwarsa, ta biyu, bayan faruwarsa.      
Ruƙya: To a wannan hanya ta biyun, za ka iya yin rukya, saboda nassin hadisin..lta kuma ruƙya wato tofi, ana yi ne da ayoyin Alƙur’ani mai girma da kuma addu’o’i da suka inganta daga bakin Annabi (ﷺ) , addu’o’in ba su ƙunshi shirka ki bidi’a ba. Wanda zai yi karatun ruƙyar (tofi) ya samu wasu halaye gwargwadon haka: Na farko mutumin da yake da cikakken tauhidi, don shi zai sa ya sami yaƙinin cewa idan an karanta za ta yi amfani. Kuma ya san cewa, ba karatunsa ba ne zai kawo sauƙin, a’a, Allah (SWA) ne zai kawo sauƙin, karatun nasa, sababi ne. Na biyu ya zamto ya iya karatun dalla-dalla. Sannan addu’ar da zai karanta, ba ta ci karo da tauhidi ba, ba kuma ta bidi'a ba, tsantsar addu’a ce daga bakin Annabi (ﷺ) . Ba kuma ƙur’ani za a canza ba, ya ce a faro daga Yasin mai rubas (wato da-baya-da-baya), ko a ce karanta Yasin, idan ka zo mubim na farko sai ka koma daga farko sai kuma ka je mub'in na biyu, haka-haka har ka sauke surar. Wannan duk kaucewa turbar Annabi (ﷺ)  ne. Nau’i ne na sihiri, don ba Alƙur’ani daidansa ake karantawa ba.
Sannan abin da ake so shi ne hucin bakin mai karatun yana samun wajen ciwon, ba wai yawu dinsa ba. Sannan za ka iya yin addu’ar sau ɗaya, ko biyu ko yadda ka ga buƙatar yin. Wani idan ya yi sau ɗaya ya wadatar, wani sai ya yi sau biyu, wani uku ko bakwai, ko goma. Ya danganci ƙarfin imanin mutum.
Don haka, akwai bambanci tsakanin kambun-baka da maita. Domin mai kambun-baka ba da niyya yake yi ba, shi kuwa maye, matsafi ne, kuma da niyya yake kama mutum. Domin mayu suna amfanuwa idan sun yi maita, shi kuwa mai kambun-baka, ba ya amfanuwa da komai idan wani ya faɗi. Sannan galibin mayu za ka ga ba sa sallah! Da mayu, da bokaye da ‘yan tsibbu galibi za ka ga aljanu sun shar’anta musu rashin yin sallah, saboda haka ne shi aljani zai biya musu bukatunsu, zai sato musu kuɗi, ko ya shiga tsakanin miji da mata Idan mutum yana so a raba wani miji da mata, sai ya sa aljani ya dunga yawo da wani wari ko ɗoyi kusa da matar, ta yadda da mijin ya z0 kusa da ita sai ya ji warin, sai ya ɗauka matarsa ce. Nan ko aljani ne, ba a ganinsa. Haka zai ta yi har sai mijin ya saki matar. Duk waɗannan (masu duba, da tsibbu, da mayu) duk mushirikai ne. Amma a yau a ƙasar Hausa, su ne malamai. Ka ji wani ɗan siyasa yana cewa, ‘ai na je wajen wani malami’ nan ko wajen mushiriki ya je! Buƙatar shi ne, bokan, ko ɗan duban ya musulunta ba ma ta maganar malinta ake ba. -
Sai dai muna da hadisin da Abdullahi ibn Abbas ya ba mu daga Annabi (ﷺ)  ya ce, “An bijiro min da al’ummomi, sai na ga wani Annabi, tare da shi akwai mutane (waɗanda ba su fi uku zuwa tara ba). Na ga wani Annabin tare da shi akwai muturn ɗaya tal, wani Annabin mutum biyu ne tare da shi. Haka kuma na ga wani Annabin babu kowa a tare da shi. Ina nan a haka, sai aka nuno min wani duhu-duhu mai girma. Sai na yi zaton al’ummata ce, sai aka ce da ni, “Wannan Musa ne da al’ummarsa.” Sai na duba, sai na ga taron mutane masu yawa, sai aka ce da mi, “Waɗannan su ne al’ummarka, a cikinsu akwai mutum dubu saba’in za su shiga aljanna ba tare da hisabi ko azaba ba.” Sannan sai ya miƙe (ﷺ)  ya shiga gidansa, sai mutane suka yi ta tattaunawa a kan waɗannan da za su shiga aljanna. Wasu suka ce, “Watakila su ne waɗanda suka aboci Manzon Allah (ﷺ) ” Wasu kuma suka ce, “Wataƙila su ne waɗanda aka haife su cikin musulunci, ba su yi wa Allah shirka ba.” Suka rinka faɗin abubuwa, Sai Annabi (ﷺ)  ya fito zuwa gare su, suka ba shi labarin tattaunawarsu, sai ya ce, “Su ne waɗanda ba sa neman a yi musu tofi, kuma ba sa yin sakiya, kuma ba sa camfa tafiyar tsuntsaye (wajen aikata wani abu, ko ƙin aikatawa), kuma suna dogara ne ga Allah shi kaɗai.” Sai Ukkashatu bin Muhsin ya tashi ya ce, “Ka roƙar min Allah ya sanya ni cikinsu.” Sai (Manzon Allah) ya ce “Kana cikinsu.” Sai wani mutum daban shi ma ya miƙe ya ce, “Ka rokar min Allah ya sanya ni cikinsu.” Sai ya ce, “Ukkashatu ya riga ka.(¹)[Bukhari #5752]
_____________
SHARHI;
(¹) Wasu malamai suka ce, “Yaushe ne aka bijiro wa Annabi al‘umma?" Wasu suka ce, a lokacin da Annabi ya yi Isra’i, wasu kuwa suka ce, a mafarki, domin mafarkin Annabawa gaskiya ne.

“...Wani Annabin babu kowa a tare da shi...” Wannan shi yake nuna ashe gaskiya ana gane ta ne ta hanyar nassi ba ta yawan mabiya ba! Yanzu ga shi duk iya wa’azi na Annabi, amma mutanen da suka yi imani ba su fi mutum tara ba. Wani kuma mutum biyu, wani ɗaya, to wani ma babu! Tare da haka wannan ya Kwacewa Annabawan gaskiyarsu? Don haka kar ka ruɗu da taron yuyuyu, a’a, taron masu hujja!

Laa yastarƙuna: Ba sa neman a yi musu tofi. Idan abu ya kama na yin tofi, sai dai su yi da kansu ko su ƙi yi. Akwai ruwayar da ta ce, “Laa yastarƙuna wa laa yarƙuna. ”cikin Muslim. Ibn Taimiyya ya ce, “Mai ruwaya ne ya ƙara wannan kalma, asalin abin da Annabi ya ce, laa  ce, laa yastarƙuna bai ce ba laa yarƙuna. Domin idan an ce, laa yarkuna-ba sa yi, ba za su yi wa kansu ba, kuma ba za su yi wa waninsu ba. Amma idan aka ce, laa yastarƙuna-ba sa neman a yi musu. Ta iya yiwuwa su yi wa wani ko kansu, amma su nemo wani su ce ka yi mini, ba za su yi ba, saboda idan su kai haka sun roƙi wani abu a wajen wani ba Allah ba. Sai dai su yi shiru.
Wa laa yaktawuna: Ba sa yin sakiya. Wani abu ya kama, sai an yi sakiya kafin a samu sauƙi, kamar maruru ko wani abu. Dangane da sakiya, hadisai sun nuna Annabi (ﷺ)  ya yi, ya yi wa wani, waɗansu kuwa sun nuna Annabi ya hana kuma ya yi izini da a yi, kamar yadda Ibnul Kayyim ya faɗa a cikin littafin Zadul-Ma’ad [4/58], ya ce, “Abubuwa guda huɗu hadisan suke nunawa. Annabi ya yi, ya hana, ya nuna ba ya so, ya yi izini da a yi.” Duk hadisan ba sa cin karo da juna. Abin da yake iya fltowa fili a nan, shi ne aikatawarsa a aikace, don ya nuna halacci ne; haninsa a nan, ba ya nuna haramci, sai dai barin sa shi ne ya fi kyau; cewar ba ya so a yi, yana nuna rashin yin sa ya fi yin sa; barin wani ya yi, yana nuna halaccinsa. Don haka, idan mutum wani abu ya kama shi na a yi masa sakiya, idan ya yi sakiya bai yi laiil ba, sai dai ya rage wa kansa falala, amma don ya yi, bai yi zunubi ba
Wa laa yata ɗayyaruna: Asalinsa sun ciro shi ne daga kalmar Aɗɗair. Don Larabawa sun kasance suna camfa tsuntsaye a wajen tashinsu ko kukansu, sukan camfa kukan wasu tsuntsaye. Idan mutum zai yi tafiya ko zai kulla kasuwanci ko auratayya, da daddare, sai ya ji kukan mujiya, sai ya fasa, babu alheri kenan. Ko kuma da sassafe sai ya zo ya sami tsuntsaye kafin su tashi, ya sami bishiyarsu, ya karkaɗa reshensu don su tashi. Da sun tashi, aka yi sa’a suka yi dama, to akwai sa’a kenan. Idan aka yi rashin sa’a suka yi hagu, sai ya fasa, don babu sa’a cikin abin kenan. Duk wannan yana cikin at-taɗayyur. To, abin yana iya cigaba, ya zamanto ko da ba da tsuntsaye aka yi amfani ba, shi ma ya zama cikin attaɗayyur: Shi ne misali, ka wayi gari, sai aka yi rashin sa’a ka fara haɗuwa da kuturu, sai a ce an yi rashin sa’a, ko ka ci karo da makaho, sai ka ce, “ai yau ba sa’a, tun da aka ci karo da makaho.” Ko mutum yana kasuwanci kuma harka tana garawa, sai ya auro mace. A ranar da ta tare, washegari sai aka kama motarka da kaya a cike, sai ya jingina wa matar. Ya ce dama tana da harara-garke. Sai a ce, ai tun da ya auro matar yake ta samun matsala. Ga shi yana ciwon kai, rannan an kama motarsa, kuma yana tafiya ya buge wani a mota. Don haka, duk yadda aka yi matar nan ce. saboda haka, sai ya sake ta hankali zai kwanta. Wannan ma duk da ba da tsuntsaye aka yi ba, amma zai shiga cikin ma‘anar. Jingina wani abu na alheri ko kishiyarsa ga tsuntsaye ko wani mutum, ya zama Ar-taaɗayyur. To su waɗannan bayin, laa yata ɗayyaruna-wato ba sa camfi. Sai dai akwai hadisin Aisha (RA) da ya zo wanda yake nuna cewa, idan ma har akwai shu’umci a cikln wani abu, to a cikin abubuwa uku ne; doki, gida, mata. Hudisin yana cikin Sahihul Bukhari (#2858, Muslim #2225]. Wannan ba yana nuna cewar za a iya yi ba ne. Sai dai Annabi (ﷺ)  ne yake ba da labarin abin da Larabawa suke yi na shu‘umci a zamanin jahiliyya. Sukan jingina wa abubuwu da dama su camfa su, amma galibi sun fi yi a kan waɗannan abubuwa uku.
wa laa rabbihim yatawakkalun: Ga Ubangijinsu kaɗai suke dogara. Dama ldan har an samu ragowar ukun, to lallai ga Allah kaɗai za a dogara.
Waɗansu malamai suka yi tattaunawa a kan me ya sa Annabi bai roƙa wa wannan mutumin ba? Sai wasu suka ce, duk da cewa adadin yana da yawa. Annubi ya ƙi haka ne don ya rufe ƙofa. Kada kowa ya tashi, shi ma ya roƙa, ko da kuwa bai cika Sharaɗin ba.

Don haka wannan hadisin ya tara abubuwa guda huɗu waɗanda sai ka cika sharuɗɗansu sannan za ku shiga cikin waɗanda za su shiga aljanna ba hisabi ba azaba.
********************
A Cikin Wannan Babi Akwai Mas’aloli Kamar haka;
1.   Gane matsayin mutane a cikin tauhidi
2.   Ma’anar tabbatar da haƙiƙanin tauhidi.
“Shi ne nisantar shirka da bidi'a da nisantar abinƙi.”

3.   Yabo daga Maɗaukaki ga Annabi Ibrahim, da cewa bai kasance cikin masu shirka ba.
4.   Yadda Allah ya yabi shugabannin waliyyan Allah saboda sun nisanci shirka.
5.   Barin neman a yi ruƙya da sakiya yana nuna tace tauhidin mutum.
6.   Kasancewar abin da yake faɗa, cewa ba sa yin tofi, sakiya da camfi, shi ne cikakken tawakkali.
7.   Zurfin ilimin sahabbai da suka gano cewa ba a samun matsayi a wurin Allah, sai da aiki.
__________
SHARHI;
Mun fahimci wannan, ƙarƙashin hadisin ta yadda, da Annabi (ﷺ)  ya ce mutum dubu sabu’in za su shiga aljanna ba azaba, ba hisabi, sahabbai ba su ce, waɗannan ‘ya’yan Annabi ba ne, ko ‘ya’yan shehi wane, ko waliyyi wane, a’a sai suka jingina abin da aiki. Sun san cewa, ba a samin matsayi dan dangantaka, sai dai ta aiki. Wannan ya nuna zurfin ilimin sahabbai kenan.

8.   Kwaɗayinsu bisa ga aikin alheri.
9.    Falalar al’ ummar Annabi (ﷺ)  ta fuskar adadi da kuma siffofi.
10.                 Falalar sahabban Annabi Musa.
11.                  Gifta al'ummomi gaban Manzon Allah (ﷺ) .
12.                 Kowace al’umma za a tashe ta, ita da Annabinta.
13.                 Ƙarancin waɗanda suke amsa wa Annabawa.
14.                 Annabin da bai samu wanda ya amsa masa ba, zai zo ranar ƙiyama shi kaɗai.
15.                 Amfanin wannan ilimin tauhidi shi ne ba a ruɗuwa da yawa da kuma rashin ƙyamatar adadi ya zama kaɗan.
16.                 Yin rangwame a kan tofi saboda kambun-baka, ko kuma cizon abu mai dafi.
17.                 Zurfin ilimin magabata (Salaf), saboda faɗinsu, “Lallai wanda ya yi aiki da ƙarshen abin da ya ji, to ya kyautata ba da son rai ba, sai dai ni ina da hadisi kaza da kaza. Sai aka fahimci cewa hadisin farko bai saɓa wa hadisi na biyu ba.
18.                 Yadda magabata suke nisantar da kansu daga yabon abin da ba su da shi.

SHARHI;
Mun fuhimci wannan a wajen da Sa‘id ibn Jubair ya tambayi ɗalibinsa cewa wa ya ga tauraro cikin dare? Ɗalibin ya ce ni ne, amma ba sallah nake ba kar ace ga waliyan Allah, ba sa barci sai sallolin dare! Ba ya san ayabe shi  da abin da ya san ba shi yake ba. Amma mutanen yanzu, so suke a yabe su da abin da ba su yi ba ma.
19.                 Faɗar Annabi (ﷺ)  cewa. “Kai kana cikinsu." alama ce da take nuna annabtar Annabi (ﷺ) .
20.                 Falalar Ukkasha.
21.                 Halaccin amfani da salon hannunka-mai-sanda a cikin magana.
22.                 Kyawawan halayen Annabi (ﷺ) .

(FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN GARIGAYI SHEIK JA’AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).  (zamuci gaba Insha Allah)

No comments:

Post a Comment

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...