GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Tuesday, November 15, 2011

ARBA'UNA HAADITH (38) HADISI NA TALATIN DA TAKWAS


An karɓo daga Abu Hurairata (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, Allah Ta'ala ya ce, "Duk wanda ya yi gaba da waliyina, to na ba shi sanarwa ya zo ya yi yaƙi da ni. Bawana ba zai kusance ni ba, da wani abu da na fi ƙauna, sama da abin da na wajabta masa. Bawana ba zai gushe ba yana kusanta ta da nafilfili, har sai na zamanto ina ƙaunarsa, idan na ƙaunace shi, sai na kasance jinsa, da yake ji da shi, da ganinsa, da yake gani da shi, da hannunsa, da yake damƙa da shi, da ƙafarsa, da yake tafiya da ita. Wallahi, idan ya roƙe ni, zan ba shi abin da ya roƙa, kuma wallahi, idan ya nemi tsarina, zan tsare shi." Bukhari ne ya rawaito shi (#6502).

SHARHI
Abin da ake nufi da waliyin Allah a nan, shi ne duk wanda yake ƙaunar Manzonsa (), mace ce ko namiji, a da ne, ko a yanzu, in dai mumini ne, mai ƙaunar Allah, to ya zama

ARBA'UNA HAADITH (37) HADISI NA TALATIN DA BAKWAI


An karɓo daga ɗan Abbas (R.A) daga Manzon Allah () cikin irin abin da ya rawaito daga Ubangijinsa, ya ce, "Allah ya riga ya rubuta ayyukan alheri da munanan
ayyuka, wanda duk ya hinmatu zai aikata wani kyakkyawan aiki, sai bai samu aikatawa ba, Allah zai rubuta masa kyakkyawan aiki guda ɗaya cikakke. Idan ya himmatu zai aikata wani kyakkyawan aiki, kuma ya aikata shi, to Ubangiji zai rubuta masa lada goma, izuwa ninki ɗari bakwai, zuwa ninkininki da yawa. In ya himmatu zai aikata mummunan aiki, kuma bai aikata ba, Allah zai rubuta masa kyakkyawan aiki cikakke a wurinsa. Idan ya himmatu da mummunan aiki, kuma ya aikata shi, Allah zai rubuta masa mummunan aiki guda ɗaya” Bukhari (#6491) da Muslim (#131) a cikin sahihan littattafansu.

ARBA'UNA HAADITH (36) HADISI NA TALATIN DA SHIDA


An karɓo daga Abu Hurairata (R.A) daga Annabi () ya ce, "Wanda duk ya kautar wa da mumini wani baƙin ciki, daga baƙin cikin duniya, to Allah zai kautar masa da wani baƙin ciki daga cikin irin baƙin cikin ƙiyama, duk wanda ya kawo sauƙi ga wanda yake cikin tsanani, Allah zai kawo masa sauƙi a duniya da lahira, wanda ya suturce musulmi, to Allah zai yi masa sutura a duniya da lahira. Lallai Allah yana cikin taimakon bawa matuƙar bawan ya kasance mai taimakon ɗan uwansa musulmi. Wanda duk ya kama wani tafarki yana neman ilimi a wannan tafarkin, Allah zai sauƙaƙa masa hanyar shiga aljanna. Babu wasu mutane da za su taru a cikin wani ɗaki cikin ɗakunan Allah, suna karanta littafin Allah, suna darasinsa a tsakaninsu da juna, face sai nutsuwa ta sauka a kansu, rahama ta lullube su, (Mala'iku sun kewaye su), sai kuma Allah ya ambacesu a fadarsa. Wanda duk aikinsa ya yi sanɗa da shi, to dangantakarsa ba za ta yi gaggawa da shi ba." Muslim ne ya rawaito shi (#2699) da Wannan lafazi.

ARBA'UNA HAADITH (35) HADISI NA TALATIN DA BIYAR


An karvo daga Abu Hurairata (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Kada ku riqa yi wa juna hassada, kada ku yi kore, kada ku yi qiyayya da juna, kada ku juya wa juna bayanku, kada sashenku ya yi ciniki a, cikin cinikin xan uwansa. Ku kasance bayin Allah, 'yan uwan juna. Musulmi xan uwan musulmi ne, kada ya zalunce shi, kada ya kunyatar da shi, kada ka yi masa qarya, kada ya wulaqantar da shi. Tsoron Allah yana nan (har sau uku)." Yana nuna kirjinsa, "Ya ishi mutum sharri, ya rinqa tozartar da xan uwansa musulmi. Jinin kowanne musulmi da dukiyarsa da mutuncinsa, haramun ne a kan musulmi“ Muslim ne ya rawaito shi (#2564).

ARBA'UNA HAADITH (34) HADISI NA TALATIN DA HUDU


An karɓo daga Abu Sa'id Alƙhuduriy (R.A) ya ce, “Na ji Manzon Allah () yana cewa, "Duk wanda ya ga abin ƙi, to ya gusar da shi da hannunsa, in ba shi da iko, ya gusar da shi da harshensa, in ba shi da iko, to ya ƙi abin a zuci, wannan shi ne mafi raunin imani" Muslim ne ya rawaito shi (#49).

SHARHI
Malamai suka ce, wannan hadisi yana cikin nassosin da ke nuna wajabcin umami da kyakkyawan aiki, da hani ga mummuna. Wannan kuma shi ne tabbatacce cikin ayoyin

ARBA'UNA HAADITH (33) HADISI NA TALATIN DA UKU


An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Da za a bai wa mutane dukkan da'awarsu, da waɗansu sun yi da'awar dukiyar waɗansu da jininsu, sai dai hujja tana kan mai da'awa, rantsuwa kuma a kan wanda ya yi musu." Baihaƙi ne ya rawaito shi a cikin littafinsa Sunan (J 10/ sh 252). Wani sashi na hadisin yana cikin Bukhari da Muslim.

SHARHI
Ma‘ana, da duk da'awar da mutane za su yi, za a ɗauka a ba su wannan abin da suka yi da'awa, misali in sun ce kaza namu ne, a ba su, ba tare da shaida ba, ba tare da an bincika

ARBA'UNA HAADITH (32) HADISI NA TALATIN DA BIYU


An karɓo daga Abu Sa'id, Sa'ad ɗan Malik ɗan Sinan Al-Khudriy (R.A) ya ce, Manzon Allah () ya ce, "Ba cuta, babu cutarwa." Ibnu Majah ne ya rawaito shi (#2341) da Daraƙuzuni (#228) da waninsu Musnadan. Haka Imamu Malik ya rawaito shi a cikin Muwaɗɗa (J2/sh 746) daga Amru ɗan Yahya daga babansa daga Annabi () Mursalan, bai ambaci Abu Sa'id ba. Amma hadisin yana da hanyoyin da sashinsu yana ƙarfafa sashi.

FASSARA DA SHARHI DAGA MARIGAYI SHEIKH JAFAR MAHAMUD ADAM (R)

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...