An karɓo
daga Abu Hurairata (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ)
ya ce, Allah Ta'ala ya ce, "Duk wanda ya yi gaba da waliyina, to na ba shi
sanarwa ya zo ya yi yaƙi da ni. Bawana
ba zai kusance ni ba, da wani abu da na fi ƙauna,
sama da abin da na wajabta masa. Bawana ba zai gushe ba yana kusanta ta da
nafilfili, har sai na zamanto ina ƙaunarsa,
idan na ƙaunace
shi, sai na kasance jinsa, da yake ji da shi, da ganinsa, da yake gani da shi,
da hannunsa, da yake damƙa da shi, da ƙafarsa,
da yake tafiya da ita. Wallahi, idan ya roƙe
ni, zan ba shi abin da ya roƙa,
kuma wallahi, idan ya nemi tsarina, zan tsare shi." Bukhari ne ya rawaito
shi (#6502).
SHARHI
Abin da ake nufi da waliyin Allah a nan, shi ne duk
wanda yake ƙaunar Manzonsa (ﷺ),
mace ce ko namiji, a da ne, ko a yanzu, in dai mumini ne, mai ƙaunar
Allah, to ya zama