An karɓo
daga Abu Abbas, Sahlu ɗan
Sa'ad Assa'idi (R.A) ya ce, "Wani mutum ya zo wajen Annabi (ﷺ)
ya ce da shi "Ya Manzon Allah! Nuna min aikin da idan na aikata shi, Allah
zai ƙaunace
ni, mutane ma za su ƙaunace ni."
Sai (Annabi ﷺ) ya ce, "Ka yi
zuhudu cikin lamarin duniya, sai Allah ya ƙaunace
ka, kuma ka nisanci abin da ke hannun mutane, sai mutane su ƙaunace
ka." Ibnu Majah ne ya rawaito shi (#4102) da waninsa ta hanyoyi masu kyau.
A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN.
GABATARWA.
WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM
WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!
DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]
Tuesday, November 15, 2011
Tuesday, November 8, 2011
ARBA'UNA HAADITH (30) HADISI NA TALATIN
An karɓo
daga Abu Sa'alaba shi ne Jursumu ɗan
Nashib (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ)
ya ce, "Lallai Allah Ta'ala ya farlanta farillai, kar ku tozarta su, ya
sanya iyakoki, kar ku ƙetare su, ya
haramta wasu abubuwa, kada ku keta alfarmarsu, ya yi shiru game da waɗansu al’amura don jinƙan
ku, ba don mantuwa ba, kar ku bincike su. Daraƙuɗuni ne ya rawaito shi a cikin littafinsa Sunan (J 4
sh 184) da waninsa.
SHARHI
Faɗin
Manzon Allah (ﷺ) cewa, "....Allah
Ta'ala ya farlanta farillai, kar ku tozarta su...." yana nufin lallai ku
tsayar da wannan farillan yadda Allah ya ɗora
muku suARBA'UNA HAADITH (29) HADISI NA ASHIRIN DA TARA
An karɓo
daga Mu'azu ɗan Jabal (R.A)
ya ce, "Na ce, Ya Manzon Allah! Ba ni labarin wani aiki da zai shigar da
ni aljanna, ya kuma nisantar da ni daga wuta.“ Sai ya ce, "Haƙiƙa
ka yi tambaya game da abin da yake mai girma, sai dai abu ne mai sauƙi
ga wanda Allah ya sauƙaƙe
shi gare shi. Ka bauta wa Allah, ba tare da ka haɗa
shi da wani ba, kuma ka tsayar da sallah, kuma ka ba da zakka, kuma ka azumci
Ramadan, sannan ka ziyarci ɗakin
Allah." Sannan sai (Annabi ﷺ)
ya ce, "Shin ba zan shiryar da kai ƙofofin
alheri ba? Azumi garkuwa ne, sadaƙa
kuma tana shafe kurakurai, kamar yadda ruwa yake kashe wuta, haka sallar mutum
a cikin yankin dare. Sannan ya karanta (faɗin
Allah), "...gefen jikinsu yana nisantar gurin kwanciyarsu. . . " har
ya kai inda (Allah yake cewa ’Ya'amaluun' sannan sai Annabi ﷺ)
ya ce, "Ba zan ba ka labarin kan al'amarin ba, da ginshikinsa da ƙololuwar
Samansa?" Sai na ce "Eh!" sai ya ce, "Kan al'amarin (shi
ne) musulunci, ginshiƙinsa kuwa salla,
ƙololuwar
samansa kuwa jihadi." (Sai Annabi ﷺ)
ya ce, "Ba zan ba ka labarin abin da yake mallakar kusan gaba ɗaya ba?" sai na ce "Ba ni labari."
sai ya kama harshensa ya ce, "Ka riƙe
wannan." Sai na ce, "Shin yanzu za a kama mu da maganar da muka
yi?" sai (Annabi ﷺ) ya ce, "Da ma
mahaifiyarka ta rasa ka! Akwai abin da yake jefa mutane wuta a kan fuskokinsu
(ko ya ce) kan hancinsu, sai sakamakon abin da harshensu ya faɗa." Tirmizi (#2616) ya ce, hadisi ne mai kyau,
ingantacce.
ARBA'UNA HAADITH (28) HADISI NA ASHIRIN DA TAKWAS
An karɓo
daga Abu Najih, shi ne Irbadu ɗan
Sariya (RA) ya ce, "Manzon Allah (ﷺ)
ya yi mana wa'azi, wa'azi mai isarwa, zukata suka tsorata, ldanu suka zubar da
hawaye. Sai muka ce da shi, "Ya Manzon Allah (ﷺ)!
Kamar wa'azin mai ban kwana? To ka yi mana wasici." Sai ya ce, "Ina
muku wasici da jin tsoron Allah, da kuma ji da bi, ko da bawa ne ya zama
shugaba a gare ku. Lallai wanda ya rayu a cikinku, da sannu zai ga saɓani mai yawa. Na umarce ku, ku riƙe
sunnata, da sunnonin halifofi shiryayyu, ku riƙe
ta da hakoranku (fiƙa), ku kiyayi
fararrun al'amura, domin kowace bidi'a ɓata
ce. Abu Dawud (#4607) da Tirmizi (#2676) suka rawaito shi, Tirmizi ya ce,
wannan hadisi ne mai kyau, ingantacce."
ARBA'UNA HAADITH (27) HADISI NA ASHIRIN DA BAKWAI
An karɓo
daga Nawas ɗan Sam'an (R.A)
ya ce, Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Aikin ɗa'a shi ne kyawawan dabi'u, laifi shi ne abin da ya
yi kai kawo a zuciyarka, kuma ba ka so mutane su ga kana yin wannan abin."
Muslim (#2553) ya rawaito.
An karɓo
daga Wabisa (R.A) ya ce, "Na zo wurin Annabi (ﷺ),
sai ya ce, "Ka zo ne kana tambaya dangane da ɗa'a?" Sai na ce, "Na‘am!" Sai ya ce,
"Ka yi wa zuciyarka fatawa,
ARBA'UNA HAADITH (26) HADISI NA ASHIRIN DA SHIDA
An karɓo
daga Abu Hurairata (R.A) ya ce, "Manzon Allah (ﷺ)
ya ce, "Dukkan gaɓɓai
na mutane akwai sadaƙa a ciki,
kowanne yini da rana ke hudowa cikinsa, da za ka sasanta tsakanin mutane biyu,
da ke rigima da juna sadaƙa ne, ka taimaki
mutum game da dabbarsa, ka ɗora
shi a kai, ko ka ɗauki
kayansa ka ɗora masa a kan
dabbar, sadaƙa ne; kalma daddaɗa sadaƙa
ce; dukkan taku da za ka yi tattaki zuwa sallah, sadaƙa
ne; ɗauke wani abu mai
cutarwa daga kan hanya sadaƙa
ne." Bukhari (#2989) da Muslim (#1009) suka rawaito shi!”
Wednesday, October 26, 2011
ARBA'UNA HADITH (25) HADISI NA ASHIRIN DA BIYAR
An karɓo
daga Abu Zarril Al Gifari (R.A) ya ce, "Waɗansu
mutane daga cikin sahabban Annabi (ﷺ)sun
ce da shi, "Ya Manzon Allah (ﷺ)!
Ma'abota dukiya sun tafi da lada, suna yin sallar (farilla) kamar yadda muke
yi, suna yin azumin (farilla) kamar yadda muke yi, amma kuma suna sadaƙa
da sauran dukiyarsu. Sai Annabi (ﷺ)
ya ce, "Shin Allah bai riga ya ba ku abin da za ku yi sadaƙa
da shi ba ne? Dukkan tasbihi sadaƙa
ne, dukkan wata kabbara sadaƙa
ce, dukkan wata hamdala sadaƙa
ce, dukkan wata hailala sadaƙa
ce, umarni da kyakkyawan aiki sadaƙa
ne, hana mummunan aiki sadaƙa
ne, a gaɓar kowanne daga cikinku
akwai sadaƙa"sai sahabbai
suka ce "Ya Manzon Allah! Yanzu mutum zai biya buƙatarsa
kuma ya zama yana da lada?" Sai (Annabi ﷺ)
ya ce, "Ku ba ni labari da a ce ya sanya (gaɓar)
tasa a cikin haram, shin yana da zunubi? To haka nan in ya sanya ta a halal zai
zama yana da lada. Muslim (#1006).
Subscribe to:
Posts (Atom)
FASSARA DA SHARHI DAGA MARIGAYI SHEIKH JAFAR MAHAMUD ADAM (R)
KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)
SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...
-
SAURARI MUQADDIMA DA SHARHIN HADISI NA (1) DAGA BAKIN MARIGAYI SHEIK JAFAR MAHMUD ADAM DOWNLOAD An karɓo daga Sarkin Muminai, baban...
-
An karɓo daga Umar (R.A) ya ce, "Yayin da muna zaune a wurin Annabi (ﷺ) wata rana, sai wani mutum ya bayyana gare mu, mai tsananin far...
-
KITABUT-TAUHID _____________ SHARHI Abin da tauhidi yake nufi shi ne kaɗait...