GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Monday, September 9, 2013

KITABUT-TAUHID (BABI NA ƊAYA 1)


                                       KITABUT-TAUHID
_____________  
SHARHI
Abin da tauhidi yake nufi shi ne kaɗaitawa, Wato daga Kalmar wahhada, Malam a nan ya na nufin Kitabut-tauhidillahi wato llttafin kaɗaita Allah. Kaɗaita Allah, kuma
ta ɓangarori ne guda uku.
  1) Rubuubiyya: Daga kalmar Rabb, wadda ma’anarta shl ne mai halitta da kuma kulawa da halitta ɗin. Tabbatarwa da Allah (SWA) ne kadai ya yi halittu gabaɗaya kuma yake kula da su, shi ne kaɗaita Allah da rububiyya.
  2) Uluuhiyya ko Al-Ilahiya: Daga kalmar A I-ilaallu wato alma ’abuudu wato abin bauta. Amma a shari’a ldan an ce alma’abuudu abin da ake nufi shi ne abin bautawa bautar ta gaske,
Don haka duk wanda aka bautawa ba Allah ba, to ba bautar gaske ba ce. Allah (SWA) kaɗai ake wa ta gaskiya. Shi ya sa kalmar shahada ta ƙunshi ɓangarori guda biyu: Bangare na farko, kwaɓe rigar ilahantaka ga kowa wato Iaa ilaaha. Sal kuma Bangare na biyu illallahu, wato sal Allah (ﷺ)  kaɗai.
 3) Kaɗaita Allah wajen sunayensa da siffofinsa. Dukkan suna ko siffa na Allah, nasa ne, wani ba ya tarayya da shi wajen sunan ko siffar.

********************
Da faɗin Allah Ta’ala;
"Kuma ban halicci aljanu da mutane ba, sai domin su bauta mini."  (Zaariyaa; 56)
__________________________
SHARHI
Malam da ya ce Kitabut-tauhid, sai ya fara da kawo ayoyi da hadisai. Wato ba ra’ayinsa ya kawo ba, zallar gaskiya ce.
        Kalmar ‘aljanu’ a ayar ta haɗa

Wednesday, March 20, 2013

KITABUT-TAUHID (SHIMFIƊA):

Tauhidi, shi ne ginshikin al’amari gabaɗaya. Domin tabbatar datauhidi ne Allah  ya saukar da Iittattafai, kuma ya turo da manzanni. Sallah, azumi, zakka, hajji, kyautatawa iyaye, kyautatawa makwabta da duk Waɗansu

Thursday, November 24, 2011

ARBA'UNA HAADITH (50) HADISI NA HAMSIN


An karɓo daga Abdullahi ɗan Busur, (R.A) yace wani mutum (mazaunin karkara ) yazo wurin Annabi (ﷺ),   yace ya Manzon Allah shari’oi sun yi mana yawa a bamu wani babu gamamme da zamu riƙe. Sai Annabi (ﷺ),  yace "kada harshenka ya bushe wajen
ambaton Allah "Ahmad ne ya rawaito shi (#188, 190).

SHARHI;

Wannan hadisin yana nuna cewa, wani mutum mazaunin karkara yazo wurin manzon Allah (ﷺ),  yace dashi ya manzon Allah shari’oi sun yi mana yawa an ce kayi kaza, ka bar kaza, don haka a faɗi wani guda ɗaya wanda zamu riƙe wanda ba gudu baja da ya sai anyi shi ko ana cikin me, Sai Annabi (ﷺ),  yace, kada harshenka ya bushe wajen ambaton Allah in dai kana son abin da zaka rike ba wahala kayi, komai kuɗinka komai talaucinka zaka iya yi ko kana da muƙami ko baka dashi kana kwance, a gadon asibiti ko a gida kake

ARBA'UNA HAADITH (49) HADISI NA ARBA'IN DA TARA


An karɓo daga Umar ɗan Khaɗɗab (R.A) daga Annabi yace, da ace kuna dogara ga Allah haƙiƙanin dogaro da Shi da Allah ya azurta ku kamar yadda yake azurta tsuntsaye. Suna sammako da yunwa amma suna dawowa
 da yamma suna ƙoshe. Imam Ahmad (# 01,52) da Tirmizi (#2344) da Nasa’i a cikin Sunnan Alkubra (J 8/ sh 79) da Ibnu Majah (#4164) da Ibnu Hibban ya inganta shi (730) da Hakin (418) Tirmizi yace, hadisi ne ingantacce.

ARBA'UNA HAADITH (48) HADISI NA DA TAKWAS


An karɓo daga Abdullahi ɗan Amru (R.A) daga Annabi (ﷺ),  ya ce, “abubuwa guda huɗu wanda suka kasance tare da shi ya kasance munafiki, wanda siffa ɗaya ta kasance tare da shi daga huɗun nan, to lallai siffa ta munafinci na tare da shi, har sai ya bar ta, idan yayi magana, ya zamanto ya yi ƙarya, Idan ya yi alƙwari, sai ya
zamanto ya saɓa, Idan an yi rigima dashi, sai ya ƙetare dokar Allah, idan kuma aka ƙulla alƙawari, to zai yaudare ka. Bukhari (#34) da Muslim(#58) suka rawaito shi.

SHARHI;


Waɗannan siffofi guda huɗu in sun taru ga mutum, to ya zama munafiki, in kuwa ɗaya ce, to wanan ya zama yana da siffa ta munafunci.To amma abin da ake nufi da munafunci a nan gurin, munafuncin aiki. Don munafunci iri biyu ne: akwai Annifaƙul Amali,

ARBA'UNA HAADITH (47) HADISI NA ARBA'IN DA BAKWAI


An karɓo daga Miƙdamu ɗan Ma'adi Yakrib (R.A) ya ce "Naji Manzon Allah (ﷺ),  yana cewa, "Dan Adam bai taɓa cika wani boki ba, ko wani ƙoƙo mafi sharri, sama da cikinsa ba. Ya ishi ɗan Adam waɗansu 'yan lomomi, wanda za su tsaida masa gadon bayansa (Yunwa ba zata galabaita shi ba). Idan dole (sai ya ci abinci da yawa), sai
ya kasa cikinsa kasha uku, kashi ɗaya abinci, kashi na biyu ruwan sha, kashi ɗayan ya bar wa numfashi."
Ahmad (J4/ sh 132) da Tirmizi (#2380) da Ibnu Majah (3349) Tirmizi ya ce, Hadisi ne mai kyau.

SHARHI;

ARBA'UNA HAADITH (46) HADISI NA ARBA'IN DA SHIDA


An karɓo daga ɗan Abu Burda, daga babansa, daga Abu Musal Ash’ariy (R.A) ya ce, Annabi (ﷺ),  ya tura shi ƙasar Yemen, sai ya tambaye shi dangane da wani abin sha da ake yi a can, sai ya ce, “Menene abin?” Sai ya ce,“Albit’u da Almizru.” sai aka ce da Abu Burda, “Menene Albit’u?” sai ya ce,
wani tsimi ne da ake yi da zuma, almizru kuwa wani tsimi ne da ake yi da alkama. Sai Annabi (ﷺ),  ya ce, “Duk abu mai sa maye haramun ne.” Bukhari ne rawaito shi (#4343).

SHARHI;


Da manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Duk abu mai sa maye haramun ne….” sai malamai suka ce abin da yake sa maye abu biyu ne: Awai abin da yake sa maye, ya kuma sa ka walwala da jin daɗi. Giya tana sa maye, tana sa walwala da jin daɗi, wani farin cikin na babu-gaira-babu-dalili. To wannan giya kenan, ittifaƙin haramun ne. Amma akwai abin da zai sa ka

FASSARA DA SHARHI DAGA MARIGAYI SHEIKH JAFAR MAHAMUD ADAM (R)

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...