GABATARWA.



WWW.TAFARKINSUNNAH.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA HADISAN ANNABI(SAW)ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;
{tafarkinsunnah@gmail.com]

Friday, November 18, 2011

ARBA'UNA HAADITH (45) HADISI NA ARBA'IN DA BIYAR

An karɓo daga Jabir ɗan Abdullahi (R.A) ya ce, “Naji Manzon Allah(ﷺ),  a shekarar buɗe Makka, a lokacin (Manzon Allah(ﷺ),  ) yana Makka, yana cewa “Lallai Allah da Manzonsa sun haramta sayar da giya da mushe da alade da gunki.” Sai aka ce, Ya Manzon Allah(ﷺ), ! Ba mu labari game da kitsen mushe, ana shafawa a jikin jirgin ruwa, ana shafawa a fata, ana kunna fitilu da shi, (shin ya halatta ko bai halatta ba?).”

ARBA'UNA HAADITH (44) HADISI NA ARBA'IN DA HUDU

An karɓo daga A’isha (R.A) ta ce, Manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Shayarwa tana haramta abin da haihuwa take haramtawa.” Bukhari (#2646) da Muslim (#1444) suka rawaito shi.

SHARHI;


Ma’ana, idan mace ta haife ka

tana da matsayin mahaifiyarka, ba ka aure ta a shari’ance; ba ka auren duk ‘yayan da ta haifa; ba ka da aurenƙannenta, domin sun zama ƙannen mahaifiyarka, ‘ya’yan da ta haifa sun zama yayayenka ko ƙannenka, ba ka auren mahaifiyata, ta zamanto kakarka. To haka matar da ta shayar da kai, ba ka aurenta  a shari’ance; ba ka auren ‘ya’yanta a shari’ance, domin sun zama yayyenka ko ƙannenka; ba ka auren

ARBA'UNA HAADITH (43) HADISI NA ARBA'IN DA UKU

An karɓo daga ɗan Abbas (R,A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Ku riskar da kowanne rabon gado sananne ga ma’abotan wannan rabon, abin da ya ragu, to a ba namiji wanda

ya fi kusanci.” Bukhari (#6732) da Muslim (#1615) ne suka rawaito shi.
SHARHI;


Abin da wanna hadisi yake nufi shi ne, rabon gado kashi biyu ne: Akawai waɗanda ake basu da farali, wato masu rabo sananne, wanda shi kuma ya kasu kashi shida: ko a ce a baka rabin dukiya (1/2), ko ɗaya bisa hudu (1/4) na dukiya, ko ɗaya bisa takwas(1/8) na dukiya, ko ɗaya bisa uku (1/3) na dukiya, ko biyu bisa ukun (2/3) na dukiya, ko ɗaya bisa

ARBA'UNA HAADITH (42) HADISI NA ARBA'IN DA BIYU

An karɓo daga Anas ɗan Malik (R.A) ya ce, “Na ji Manzon Allah (ﷺ),  yana cewa, Allah Maɗaukakin Sarki yana cewa, “Ya kai ɗan Adam! Lallai ba za ka bauta min ba, kuma ka sanya rai game da rahamata ba, face sai na gafarta maka ban damu ba. Ya kai ɗan Adam! Da a ce zunubanka zasu cika sashen sama gaba ɗaya, sannan ka nemi gafarata, sai in gafarta maka. Ya kai ɗan Adam!

Da a ce zaka zo min da cikin ƙasa gaba ɗaya zunubai ne, sannan ka gamu dani, ba tare da ka haɗa ni da kowa ba, Ni kuma zan kawo maka gafara, cikin ƙasa.” Tirmizi ne ya  rawaito shi (#3540) ya ce, hadisi ne mai kyau, ingantacce.

ARBA'UNA HAADITH (41) HADISI NA ARBA'IN DA DAYA

An karɓo daga Abu Muhammad Abudullahi ɗan Amru ɗan As (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Ɗayanku ba ya zama mumini, har sai son zuciyarsa yana biyayya ga abin da na zo da shi.” Hadisin ne ingatacce, mai kyau, mun rawaito shi a cikin littafin Hujja da sanadi ingantacce.

SHARHI;

Wanna hadisi an karɓo shi daga Abu Muhamad, shi ne Abdullahi ɗan Amru ɗan As, ɗaya daga cikin ‘Abadila’ (wato waɗanda ake kira Abdullahi ) a cikin sahabbai,
waɗanda su huɗu ne, duk sunansu ya fara Abdullahi: su ne, Abdullahi bn Umar, Abdullahi bn Abbas, Abdullahi bn Mas’ud da Abdullahi bn Amru bn As. Waɗannan

Tuesday, November 15, 2011

ARBA'UNA HAADITH (40) HADISI NA ARBA'IN


An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ),  ya dafa kafaɗata ya ce, “Ka kasance a duniya tamkar kai baƙo ne, ko kuma wanda yake kan hanya.” Ɗan Umar (R.A) yana cewa, “Idan ka kai yamma, kar ka yi jiran safiya, idan kuma ka wayi gari, to kar ka jira yamma. Ka riƙi aiki alheri lokacin lafiyarka, saboda lokain rashin lafiyarka. Ka riƙi aiki alheri lokacin rayuwarka, saboda ka
amfana lokacin mutuwarka.” Bukhari ne ya rawaitoshi. (#6416).

SHRHI;

Manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Ka kasance a gidan duniya tamkar baƙo ne…”

ARBA'UNA HAADITH (39) HADISI NA TALATIN DA TARA


An karɓo daga ɗan Abbas (R.A) ya ce Manzon Allah (ﷺ),  ya ce, “Allah Ya yafe wa al’ummata, abin da ta yi dakuskure, da mantuwa, da abin da aka tilasta ta.” Hadisi ne mai kyau Ibnu Majah ne ya rawaito shi (#2045) da Baihaƙi a cikin Sunan.

SHARHI;

Waɗannan abubuwa guda uku an yafe wa Al’ummar Annabi (ﷺ), . Kuma wannan ɗaya ne daga cikin abin da yake nuna falalarmu a kan sauran al’ummai, saboda sauran al’ummai ba a basu wannan damar ba. Mu kaɗai ne muke da irin wannan damar, don ya ce a hadisin, “Allah Ya yafe wa al’ummata…” wanan ya nuna sauran al’ummar da suka gabata, ba su sami wannan falalar ba.

FASSARA DA SHARHI DAGA MARIGAYI SHEIKH JAFAR MAHAMUD ADAM (R)

KITABUT-TAUHID (Babi Na Goma Sha Biyar15)

  SHARHI Babukan da suka wuce sun yi magana a kan yana daga dangin shirka neman taimako wajen wanin Allah. Wannan babi kuma zai nuna maka ...